Daga Wakiliya
Maganar da Uwargidan Shugaban Ƙasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta yi kan kosai, masara da kuli-kuli ta jawo cece-kuce a Najeriya. Wasu sun kare ta, suna cewa babu kunya a cikin yin sana’a, kuma mutane da dama sun fara rayuwarsu da ƙananan sana’o’i kafin su yi nasara. Wannan gaskiya ne.
Babu laifi ko kaɗan a sayar da kosai, gasa masara, yin kuli-kuli ko wata sana’a ta halal. Dubban iyalai sun gina rayuwarsu, sun biya wa ‘ya’yansu kudin karatu kuma sun samu ci gaba ta irin waɗannan sana’o’i. Duk aikin halal abin girmamawa ne.
Amma wannan ba shi ne abin da ya fusata ‘yan Najeriya ba.
Abin da ya fi damun mutane shi ne yadda ake ta gaya musu su ci gaba da jure wahala, alhali masu mulki suna rayuwa cikin walwala.
Idan tattalin arziƙin ƙasa yana tafiya yadda ya kamata, mutane za su yi magana ne kan sabbin damar kasuwanci, ayyukan yi, ilimi, lafiya, wutar lantarki da ci gaba.
Amma idan rayuwa ta yi tsanani, duk wata magana da ta shafi talauci tana zama abin cece-kuce.
Hakika, N50,000 na iya taimaka wa wasu ƙananan ‘yan kasuwa su ƙara jari. Amma akwai tambaya mai muhimmanci:
Yaya miliyoyin ‘yan Najeriya da ke cikin bashi, ba su da abin da za su ci, suna fama da kuɗin haya, sufuri, kuɗin makaranta da tsadar abinci?
Idan ana bin mutum bashin fiye da dubu N150,000, kuma yana fama da yunwa, shin dubu N50,000 zai warware matsalarsa?
Matsalar ba tallafin ba ce.
Matsalar ita ce jefa wa mutane talauci har ta kai ga hannu baka hannu kwarya kawai ake nuna wa a matsayin ci gaban tattalin arziƙi.
Abin da ‘yan Najeriya suke so ba rabon tallafi ba ne har abada.
Suna son tattalin arziƙin da yake aiki.
Suna son:
– Wutar lantarki mai ɗorewa domin kasuwanci ya bunƙasa.
– Abinci mai sauƙin samu.
– Tsaro domin manoma su koma gonakinsu.
– Ayyukan yi masu albashi mai kyau.
– Rancen kuɗi cikin sauƙi da sharudda masu kyau.
– Ƙasar da matasa za su iya yin mafarkin rayuwa mai kyau, ba rayuwar neman abin da za a ci kawai ba.
Abin da ya sa mutane da yawa suka fusata da maganar kosai ba saboda raina sana’ar kosai ba ne.
Saboda gajiya ce.
Saboda takaicin rayuwa.
Saboda mutane suna ganin ana ƙara ɗora musu wahala, amma ana rage musu buri.
Babu wanda ya ce ƙananan sana’o’i ba su da amfani.
Babu wanda ya ce a ji kunyar fara rayuwa daga ƙasa.
Abin da ‘yan Najeriya suke cewa shi ne:
A daina amfani da talauci a matsayin abin da za a saba da shi.
A daina nuna wahala kamar al’ada ce.
A daina ɗaukar rayuwar talauci a matsayin nasara.
A gina tattalin arziƙin da mutane za su sayar da kosai saboda sun zaɓa, ba saboda babu wata dama ba.
Ci gaban ƙasa ba auna shi ake yi da yadda mutane ke iya jure wahala ba.
Ana aunawa ne da yadda rayuwar jama’a take inganta, da yadda mutane ba sa fama da wahalar rayuwa kullum.
Wannan ce tattaunawar da ya kamata Najeriya ta mayar da hankali a kai.
‘Yan Najeriya sun cancanci fiye da rayuwar hannu baka hannu kwarya kawai.
Sun cancanci gwamnatin da za ta samar da dama, ta kare rayuka, ta bunƙasa kasuwanci, ta kuma dawo da bege ga jama’a.
Fassarar makalar : Odewale Adesoye (Green Man) daga Wakiliya





