Daga Wakiliya
Attajirin dan kasuwar Zimbabwe, Kudakwashe Tagwirei, ya ware dala miliyan 1 domin taimakawa gwamnatin kasarsa wajen dawo da ‘yan Zimbabwe har 20,000 daga South Africa, sakamakon karuwar fargabar hare-haren kyamar baki a kasar.
Tallafin, wanda aka bayar ta gidauniyar Bridging Gaps Foundation tare da matarsa Sandra Tagwirei, zai taimaka wajen samar da motocin bas da za su kwaso ‘yan Zimbabwe daga biranen Afirka ta Kudu zuwa kan iyakar Beitbridge Border Post, sannan a ci gaba da kai su garuruwansu a Zimbabwe.
Rahotanni sun ce daruruwan ‘yan Zimbabwe sun kwashe kwanaki suna kwana a wajen ofishin jakadancin kasarsu da ke Cape Town suna jiran a dawo da su gida, bayan karuwar fargabar tashe-tashen hankula da suka shafi bakin haure.
Matakin Tagwirei ya zo ne a daidai lokacin da kasashen Malawi da Mozambique ma suka fara shirye-shiryen dawo da ‘yan kasashensu daga Afirka ta Kudu.
Ko da yake Tagwirei na fuskantar takunkumi daga Amurka da UK kan zarge-zargen cin hanci, ya musanta aikata wani laifi, kuma ya ci gaba da gudanar da ayyukan tallafi ta gidauniyarsa.





