Kwankwaso ya fara nadamar matakin da ya ɗauka na komawa NDC -Bashir Ahmad
Daga Wakiliya
Tsohon mai taimaka wa Shugaban Ƙasa, Bashir Ahmad, ya ce yasan zuwa yanzu Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya fara yin nadamar shawarar da ya yanke ta komawa jam’iyyar NDC.
A cewarsa, wannan mataki na siyasa ya janyo wa Kwankwaso asarar tasirin siyasar da ya taɓa samu a Jihar Kano, inda ya kasance yana da gagarumin karfin siyasa, amma yanzu ba bu.
Bayanan na Bashir na zuwa ne bayan ficewar galibin jiga-jigan NDC kuma na kusa-kusa da Kwankwaso da suka sauya sheka daga NDC zuwa APC kuma suka fice daga tafiyar Kwankwasiyya




