Daga Wakiliya
Kotun Tarayya da ke Abuja ta tabbatar da halaccin shugabancin jam’iyyar ADC Æ™arÆ™ashin jagorancin Sanata David Mark, tare da yin watsi da Æ™arar da É—an majalisar wakilai, Leke Abejide, ya shigar yana Æ™alubalantar shugabancin jam’iyyar.
Mai shari’a Musa Liman ya ce kotu ba ta da hurumin tsoma baki cikin harkokin cikin gida na jam’iyya, sannan ya bayyana cewa Abejide bai bi hanyoyin sasanta rikici na cikin jam’iyyar ba kafin ya garzaya kotu.
Kotun ta kuma yanke cewa naÉ—in David Mark a matsayin shugaban jam’iyyar da kuma Rauf Aregbesola a matsayin sakatare ya gudana ne bisa kundin tsarin mulkin jam’iyyar da kuma Dokar ZaÉ“e ta 2026.
Haka kuma, kotun ta ci tarar Abejide Naira miliyan 2 ga kowane ɗaya daga cikin waɗanda ya ƙara, sannan ta ci lauyansa Naira miliyan 10 saboda shigar da ƙarar.
Abejide dai ya nemi kotu ta soke mika ragamar shugabancin ADC daga tsohon shugaban jam’iyyar, Ralph Nwosu, zuwa David Mark da Aregbesola, tare da hana INEC amincewa da su, amma kotu ta yi fatali da dukkan buÆ™atunsa.
Wakiliya | Muryar Arewa a Duniya





