Daga Wakiliya
Babbar Kotun Jihar Kaduna ta sake yin watsi da bukatar bayar da belin tsohon gwamnan jihar, Nasir Ahmad El-Rufai, a shari’arsa da ICPC
Mai shari’a D. H. Khobo ya yanke hukuncin ne bayan El-Rufai ya nemi a bayar da shi beli bisa dalilin rashin lafiya, yana mai gabatar da wata takarda da aka ce ta fito daga babban Asibitin Abuja, wato Abuja National Hospital.
Sai dai ICPC ta gabatar da martani daga Babban Daraktan Asibitin, Muhammad Raji Mahmud, wanda ya bayyana cewa binciken da aka yi bai gano wata shaida da ke nuna El-Rufai ya taba samun magani a asibitin ba, tare da cewa takardar ba ta samu amincewar mahukuntan asibitin ba.
Kotun ta ce bayan an karyata ingancin takardar, babu wata hujja mai karfi da za ta tabbatar da bukatar belin saboda rashin lafiya, don haka ta yi watsi da bukatar.
Sai dai kotun ta umarci ICPC da ta ci gaba da bai wa El-Rufai damar ganin likitocinsa tare da raka shi zuwa duk wata cibiyar lafiya ta musamman da ya zaba a cikin Najeriya idan bukatar hakan ta taso yayin da ake ci gaba da shari’ar.
ICPC ta ce ta yi maraba da hukuncin, tana mai jaddada cewa za ta ci gaba da gudanar da bincike da shari’o’inta cikin adalci da bin doka.





