Ko Maƙiyina Zai Shaida Cewa Kano Tawa Ce – Kwankwaso Ya Yi Martani Ga Ali Modu Sheriff

Daga Wakiliya


Dan takarar mataimakin shugaban ƙasa na jam’iyyar NDC, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, ya yi watsi da kalaman tsohon gwamnan Borno, Ali Modu Sheriff, wanda ya ce haɗakarsa da Peter Obi ba za ta samu karɓuwa a Kano da sauran Arewacin Najeriya ba.

Kwankwaso ya bayyana a wata hira da tashar Channels TV cewa ƙarfin siyasarsa a Kano abu ne da kowa ya sani, har ma da abokan hamayyarsa.

Ya ce Ali Modu Sheriff ya faɗi hakan ne kawai domin ya nuna wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu cewa yana yi masa aiki.

> “Ko maƙiyina mafi tsanani zai gaya maka cewa Kwankwaso yana da Kano. Ba na daga cikin ‘yan siyasar da ke yawan taƙama. A maimakon haka, ina farin ciki idan mutane suka raina ƙarfinmu, saboda hakan yana sa su yi sakaci yayin da muke ci gaba da aiki,” in ji Kwankwaso.



Tsohon gwamnan Kano ya kuma bayyana cewa haɗin gwiwar Kwankwasiyya da magoya bayan Peter Obi (Obidients) zai kawo manyan sauye-sauye a siyasar Najeriya kafin zaɓen 2027.

Kwankwaso ya ƙara da cewa Peter Obi ba sabon ɗan takara ba ne a Arewacin Najeriya, yana mai tunatar da cewa ya samu sama da ƙuri’u miliyan biyu a yankin a zaɓen da ya gabata.

A cewarsa, haɗakar magoya bayan Obi da Kwankwasiyya za ta ba da mamaki musamman daga matasa, waɗanda ya ce ba sa damuwa da siyasar rarrabuwar kawuna da wasu ke ƙoƙarin yadawa.

DA DUMI-DUMI

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Kanun Labarai

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Shaida Mata Zai Auri Wata – Rundunar Yan Sanda

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Sanar da Ita Cewa Zai Auri Wata — Rundunar 'Yan Sanda

Mata Sun Fi Maza Cika Alƙawarin Biyan Bashi – Inji Rahoton Moniepoint

Moniepoint ta ce alkaluman sun nuna cewa, duk da matsalolin da mata ke fuskanta wajen samun rance saboda buƙatar jingina ko rashin tarihin bashi, suna daga cikin rukunin masu kasuwanci da suka fi nuna amana wajen biyan bashin da suka karɓa.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img