Kamfanin Amurka dake binciken zargin fataucin miyagun ƙwayoyin Tinubu ya ce an yi masa tayin cin hancin Dala miliyan $3m don ya daina bibiyar lamarin

DA DUMI-DUMI

Kamfanin Amurka dake binciken zargin fataucin miyagun ƙwayoyin Tinubu ya ce an yi masa tayin cin hancin Dala miliyan $3m don ya daina bibiyar lamarin

Daga Wakiliya

Wani kamfanin ba da shawarwari kan harkokin siyasa da lobbi da ke Amurka, Von Batten-Montague-York, ya ce ya kai wa Ma’aikatar Shari’a ta Amurka (DOJ) rahoton wani tayin cin hancin dala miliyan uku ($3m), Kimanin Naira Biliyan 4bn.

Kamfanin ya ce an yi tayin ne domin dakatar da binciken da ake zargin yana da alaƙa da Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, kan zargin fataucin miyagun ƙwayoyi.

A wani saƙo da kamfanin ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis, ya ce shugaban kamfanin, Dr Von Batten, ya ƙi amincewa da tayin, tare da adana kwafin saƙonnin da aka aika masa.

Kamfanin ya ce saboda girman kuɗin da aka ambata, da kuma shawarar gudanar da wata ganawa ta sirri a Landan, tare da amfani da saƙonnin (view once) da ke ɓacewa, ya ga ya dace ya kai lamarin ga hukumomin Amurka.

Ya ce ya kuma miƙa hotunan (screenshots) na saƙonnin da aka tura masa ga ma’aikatar Shara’a ta Amurka,  DOJ.

Kamfanin ya ƙara da cewa yanzu zai bar Ma’aikatar Shari’ar Amurka ta tantance ko saƙonnin sun isa a buɗe wani ƙarin bincike.

Sai dai zuwa yanzu ba a bayyana wanda ya yi tayin kuɗin ko kuma ko DOJ ta fara wani bincike a hukumance kan lamarin ba.

- Advertisement -spot_img

Leave a Reply

- Advertisement -spot_img
Za ku so wadannan

Gwamnatin Najeriya za ta fara biyan tsoffin ma’aikatan Nigeria Airways Naira biliyan 18

Sai dai ya bayyana cewa gwamnati za ta biya kuɗin da aka tantance kuma aka tabbatar da shi, ba tare da ƙarin kuɗin da ya dace da hauhawar farashi na tsawon shekaru 20 ba.
- Advertisement -spot_img

Labarai masu alaka

- Advertisement -spot_img