Intanet ta zama sabon filin yaƙi da ‘yan ta’adda ke amfani da shi, suna ɗaukar sabbin mambobi da tara kuɗi

‘Yan ta’adda na amfani da intanet wajen ɗaukar sabbin mambobi, tara kuɗi – Rundunar Sojin Najeriya

Rundunar Sojin Najeriya ta yi gargaɗin cewa ‘yan ta’adda da sauran ƙungiyoyin masu aikata laifuka na ƙara amfani da intanet wajen ɗaukar sabbin mambobi, yaɗa farfaganda, tara kuɗi da kuma tsara hare-hare, lamarin da ta ce na ƙara barazana ga tsaron ƙasa.

Babban Hafsan Sojin Ƙasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya bayyana hakan a taron 2026 Nigerian Army Cyber Warfare School Seminar da aka gudanar a Abuja.

Ta bakin Mataimakin Babban Hafsan Sashen Ayyuka na Musamman, Manjo Janar Jeremiah Manjang, Shaibu ya ce intanet ta zama sabon filin yaƙi, inda maƙiya ke amfani da fasahar zamani ba tare da kasancewa a wurin ba wajen kai hare-hare, satar bayanai da yaɗa bayanan ƙarya.

Ya ce ‘yan ta’adda, masu garkuwa da mutane, ‘yan bindiga da sauran masu aikata laifuka na amfani da kafafen intanet wajen ɗaukar sababbin mambobi, tara kuɗi, tattara bayanan sirri da kuma ɓoye mu’amalolin kuɗaɗen da suka samu ta haramtacciyar hanya.

Shaibu ya ce hakan na buƙatar haɗin gwiwa tsakanin gwamnati, hukumomin tsaro, masana da kamfanoni masu zaman kansu domin ƙarfafa tsaron yanar gizo da kare muhimman cibiyoyin Najeriya.

Ya kuma buƙaci a ƙara saka hannun jari wajen bunƙasa fasahar cikin gida, amfani da basirar wucin gadi (AI) da kuma horas da ƙwararrun ma’aikata domin ƙarfafa kariyar dijital da tsaron ƙasa.

Shi ma Kwamandan Nigerian Army Cyber Warfare School, Birgediya Janar Jacob Bawa, ya ce ƙaruwar amfani da fasahar dijital ta sa cibiyoyi masu muhimmanci kamar sadarwa, lantarki, bankuna da bayanan gwamnati suka fi fuskantar barazanar hare-haren intanet.

A nasa jawabin, ƙwararren masanin tsaron yanar gizo Abdulhakeem Ajijola ya ce Najeriya na buƙatar gina nata ƙarfin tsaron intanet, yana mai gargaɗin cewa dogaro da manhajoji da fasahohin ƙasashen waje kaɗai na iya zama barazana ga tsaron ƙasa.

DA DUMI-DUMI

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Kanun Labarai

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Shaida Mata Zai Auri Wata – Rundunar Yan Sanda

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Sanar da Ita Cewa Zai Auri Wata — Rundunar 'Yan Sanda

Mata Sun Fi Maza Cika Alƙawarin Biyan Bashi – Inji Rahoton Moniepoint

Moniepoint ta ce alkaluman sun nuna cewa, duk da matsalolin da mata ke fuskanta wajen samun rance saboda buƙatar jingina ko rashin tarihin bashi, suna daga cikin rukunin masu kasuwanci da suka fi nuna amana wajen biyan bashin da suka karɓa.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img