Daga Wakiliya
Hukumar ZaÉ“e Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta ce tana shirin cire jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) daga jerin jam’iyyun siyasa da aka yi wa rajista, bayan wata sabuwar hukuncin Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta soke umarnin da ya tilasta wa hukumar yin mata rajista.
Jam’iyyar NDC dai ita ce wacce Peter Obi da Rabiu Kwankwaso ke yi wa takarar shugaban kasa da mataimaki a babban zaben 2027
Kwamishinan INEC mai kula da yaɗa bayanai da wayar da kan masu zaɓe, Mohammed Kudu Haruna, ya bayyana cewa hukumar ta nemi kwafin cikakken hukuncin kotun (CTC), kuma za ta aiwatar da abin da kotun ta yanke da zarar ta karɓe shi.
A ranar Juma’a ne Mai Shari’a Isah Dashen ya soke hukuncin da kotun ta yanke a ranar 10 ga Disamba, 2025, wanda ya umarci INEC ta yi wa NDC rajista.
Tun da farko dai wata kungiya ce mai suna Peace Movement Party ta shigar da kara tana kalubalantar cewa alamar tambarin jam’iyyar NDC ya yi kama da nata. Don haka ta zargi NDC da yi mata satar fasaha (tambari/logo).
Lauyan PMP, C. S. Ekeocha, ya ce hukuncin ya mayar da komai yadda yake kafin ranar 10 ga Disamba, 2025, wanda ke nufin duk wata amincewa da aka bai wa NDC, takardar rajistarta da kuma saka sunanta cikin bayanan INEC za a janye su har sai an kammala sauraron shari’ar.
Sai dai ya jaddada cewa har yanzu ba a yanke hukunci kan ainihin shari’ar ba, domin za a ci gaba da sauraronta bayan an haÉ—a dukkan É“angarorin da abin ya shafa.





