Daga Wakiliya
Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Najeriya (ICPC) ta zargi tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Mallam Nasir Ahmad El-Rufai, da amfani da damar da kotu ta ba shi ta zuwa duba lafiya wajen gudanar da abin da ta ce ya sabawa manufar umarnin kotu.
A cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta ce kotun jihar Kaduna ta ware ranakun 6, 7 da 8 ga Yulin 2026 domin ci gaba da sauraron shari’ar da ake yi wa El-Rufai, amma bai halarci zaman farko ba saboda ya bukaci ganin likitansa na kashin kai.
ICPC ta ce, duk da cewa ta amince da bukatar bisa umarnin kotu tare da samar da tsaro, jami’anta sun gano hotuna da wani abokin siyasar El-Rufai, Isa Ashiru Kudan, ya wallafa a Facebook, yana cewa sun gana da El-Rufai a lokacin da ake zargin yana dakin ganin likita.
Hukumar ta ce hotunan sun nuna cewa an yi amfani da ziyarar asibitin wajen gudanar da wasu ayyuka da ba su cikin abin da kotu ta amince da shi, lamarin da ta bayyana a matsayin karya umarnin kotu.
ICPC ta kuma sanar da cewa ta kama likitan El-Rufai, Farfesa Bello Abubakar, domin gudanar da bincike, tana zarginsa da bayar da bayanan karya.
Hukumar ta ce za ta sanar da kotu abin da ta kira rashin bin umarnin kotu da El-Rufai ya yi, tare da jaddada cewa za ta ci gaba da gudanar da aikinta bisa doka, kuma ba za ta amince da cin zarafin kyakkyawar niyyarta daga kowane mutum ko kungiya ba.
Har zuwa lokacin wallafa wannan labari, Mallam Nasir Ahmad El-Rufai ko lauyoyinsa ba su fitar da martani kan zargin da ICPC ta yi ba.





