Daga Wakiliya
Hukumar Kula da Ma’aikatan Shari’a ta Jihar Kano (Judicial Service Commission – JSC) ta tilasta wa Alƙalin Kotun Shari’a da ke Babeji, Aliyu Yahaya Muhammad, yin ritaya bayan ta same shi da laifin karɓar cin hancin N250,000 a wata shari’a.
A cikin sanarwar da kakakin ma’aikatar shari’ar jihar, Baba Jibo Ibrahim, ya fitar, ya ce an yanke hukuncin ne a taron JSC na 90 bayan binciken Kwamitin Karɓar Korafe-korafen Jama’a ya tabbatar da zargin.
Hukumar ta kuma umarci Aliyu Yahaya Muhammad da ya mayar da kuɗin N250,000 da aka ce ya karɓa.
Haka kuma, magatakardar kotun, Ibrahim Ahmad Ibrahim, ya samu dakatarwa na tsawon watanni huɗu ba tare da albashi ba, bayan ya amsa cewa ya karɓi wani ɓangare na kuɗin cin hancin.
A wani hukuncin daban, JSC ta tilasta wa Muzambilu Ado, Mukaddashin Daraktan Hulɗa da Jama’a da Kididdiga na Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Shari’a, yin ritaya bayan bincike ya gano cewa ya gabatar da takardun karatu na bogi wajen samun aiki.
Sannan hukumar ta rage wa Alƙalin Babbar Kotun Shari’a ta Goron Dutse, Usman Haruna Usman, matsayi da mataki ɗaya saboda sakaci da ya haifar da asarar kuɗaɗen masu ƙara, tare da tabbatar da dakatarwar da aka yi masa na shekara guda daga aikin shari’a.
Baba Jibo Ibrahim ya ce matakan da aka ɗauka sun nuna ƙudirin JSC na tabbatar da gaskiya, riƙon amana da ɗa’a a harkokin shari’a, yana mai jaddada cewa duk wani jami’in shari’a da aka samu da laifin cin hanci ko amfani da ofis ba daidai ba zai fuskanci hukuncin da ya dace.





