Daga Wakiliya
Gwamnatin Tarayya ta jaddada aniyarta ta aiwatar da sabuwar Dokar Hukumar Kula da Shaidar Ɗan Ƙasa (NIMC) ta 2026, wadda ta tanadi amfani da Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa (NIN) a matsayin babbar kuma guda ɗaya da za a riƙa amfani da ita wajen tantance ‘yan Najeriya.
Ministan Kasafi da Tsare-tsaren Tattalin Arziki, Abubakar Bagudu, ya bayyana hakan yayin ganawa da Darakta Janar ta National Identity Management Commission, Abisoye Odusote, a Abuja.
Bagudu ya ce sabuwar dokar za ta ƙarfafa tsarin shaidar dijital na Najeriya, ta inganta shugabanci da kuma samar da ingantattun bayanai da za su taimaka wajen tsara manufofin ci gaba.
Ya kuma buƙaci haɗin gwiwa tsakanin gwamnatin tarayya, jihohi da ƙananan hukumomi domin kawo ƙarshen yawaitar bayanan shaida daban-daban, tare da tabbatar da cewa NIN ta zama shaidar da za a amince da ita a ko’ina cikin ƙasar.
A nata ɓangaren, Darakta Janar ta NIMC, Abisoye Odusote, ta bayyana cewa sabuwar dokar ta soke wadda aka kafa a shekarar 2007, tare da tabbatar da tsarin “mutum ɗaya, shaida ɗaya”, sannan ta ƙara matakan kariyar bayanai da inganta tsarin dijital na ƙasa.





