Daga Wakiliya
Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya sanar da yin murabus daga mukaminsa na Firaminista da kuma shugaban jam’iyyar Labour.
A jawabin da ya gabatar a gaban gidan gwamnati na 10 Downing Street, Starmer ya ce ya fahimci cewa jam’iyyarsa ba ta ganin shi ne ya fi dacewa da jagorantar ta zuwa babban zaÉ“e mai zuwa.
Ya bayyana cewa zai ci gaba da riÆ™e mukamin har sai an zaÉ“i sabon shugaban jam’iyyar domin tabbatar da mika mulki cikin tsari.
Starmer ya gode wa iyalansa, musamman matarsa Victoria, tare da bayyana cewa nasarar dawo da Labour kan mulki ita ce mafi girman nasara a rayuwarsa ta siyasa.Rahotanni na nuna cewa Andy Burnham na daga cikin waÉ—anda ake hasashen za su maye gurbinsa a shugabancin jam’iyyar Labour.





