Daga Wakiliya
Kotun Tarayya da ke Abuja ta sake nuna bidiyon hirar tsohon Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai, da ya yi a Arise TV yayin da lauya kuma mai rajin kare haƙƙin ɗan Adam, Deji Adeyanju, ya bayar da shaida a shari’ar da Hukumar DSS ke yi masa.
Adeyanju ya shaida wa kotun cewa bidiyon ya nuna abubuwan da ya gani da kunnensa a shirin da aka gudanar ranar 13 ga Fabrairu, inda El-Rufai ya yi ikirarin cewa ya samu bayanai daga wata tattaunawar wayar tarho da ta shafi Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa Shawara Kan Tsaro, Nuhu Ribadu.
A yayin tambayoyi daga lauyoyin ɓangarorin biyu, Adeyanju ya ce El-Rufai ya furta cewa “sun saurari kiran wayoyinsu”, amma bai ce da kansa ya yi kutse ko ya sace wayar ba.
DSS na tuhumar El-Rufai da laifin sauraron ko kutse cikin tattaunawar wayar Ribadu ba bisa ƙa’ida ba. Tsohon gwamnan ya musanta zarge-zargen kuma yana fuskantar shari’a kan tuhume-tuhume guda biyar.Bayan kammala zaman ranar Litinin, Mai Shari’a Joyce Abdulmalik ta ɗage sauraron ƙarar zuwa ranar Talata domin ci gaba da shari’ar.





