Daga Wakiliya
Hukumar EFCC ta ce ta kwato fiye da Naira biliyan 38.66, kuɗaɗe da kadarori, yayin binciken zargin karkatar da kuɗaɗen da aka ware domin gyaran matatun mai na Port Harcourt, Warri da Kaduna.
Rahotanni sun nuna cewa an kwato Naira biliyan 9.4, da kuma dala miliyan 21.2, baya ga wasu filaye da kadarori da ake zargin an mallaka da kuɗaɗen da aka karkatar.
Ana zargin wasu tsofaffi da na yanzu daga NNPCL, shugabannin matatun mai da kuma wasu kamfanonin kwangila da hannu wajen karkatar da kuɗaɗen gyaran matatun, duk da cewa gwamnatin tarayya ta kashe kusan dala biliyan 2.8 kan aikin.
EFCC ta bayyana cewa binciken na ci gaba, kuma ana sa ran ƙarin ƙwato kadarori tare da gurfanar da waɗanda ake zargi a gaban kotu.





