Daga Wakiliya
Jam’iyyar Nigeria Democratic Congress (NDC) ta ce Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta ƙi ba ta lambar sirri (Access Code) da za ta yi amfani da ita wajen ɗora sunayen ‘yan takararta a shafin hukumar gabanin zaɓen 2027.
Mai magana da yawun jam’iyyar, Osa Director, ya ce sun nemi lambar daga INEC amma har yanzu ba su samu amsa ba. Ya ƙara da cewa jam’iyyar za ta garzaya Kotun Ɗaukaka Ƙara domin ƙalubalantar hukuncin da Babbar Kotun Tarayya da ke Lokoja ta yanke, wanda ya umarci INEC da kada ta amince da NDC har sai an kammala shari’o’in da ke kanta.
A nata ɓangaren, shugabannin NDC sun dage cewa jam’iyyar tana nan a matsayin halastacciyar jam’iyya, kuma za ta tsaya takara a zaɓen 2027.
Shugaban jam’iyyar, Sanata Moses Cleopas Zuwoghe, ya ce hukuncin kotun bai soke rajistar NDC ba, yana mai tabbatar da cewa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar, Peter Obi, da sauran ‘yan takara za su kasance a takardar zaɓe idan an kammala shari’ar.





