DSS ta saki wani Dan Arewa da ta tsare bisa kuskure kan zargin alaƙa da Boko Haram, ta ba shi diyyar Naira miliyan 3m

Daga Wakiliya


Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta saki wani manomi kuma makiyayi, Nura Idris, bayan wani bincike na cikin gida ya tabbatar da cewa babu wata hujja da ke nuna yana da alaƙa da ƙungiyar Boko Haram.

Rahotanni sun ce Darakta Janar na DSS, Oluwatosin Ajayi, ne ya bayar da umarnin a sake shi tare da ba shi diyyar gaggawa ta Naira miliyan uku domin rage masa raɗaɗin abin da ya fuskanta.

An kama Nura ne a watan Yunin 2024 a Suleja, jihar Neja, bisa zargin ta’addanci, kafin daga bisani a miƙa shi ga DSS.

Majiyoyi sun bayyana cewa bayan sake nazarin shari’arsa, jami’an binciken DSS sun gano babu wata hujja da ke tabbatar da zargin da ake masa.

Baya ga diyyar kuɗi, DSS ta yi alƙawarin taimaka masa wajen farfaɗo da harkokin kiwon dabbobi domin ya ci gaba da rayuwarsa.

Rahotanni sun kuma ce hukumar na ba wa waɗanda aka wanke daga irin waɗannan zarge-zarge tallafin jinya, kula da lafiyar ƙwaƙwalwa da kuma taimakon sake komawa rayuwa.

An ce sakin Nura na daga cikin shirin DSS na sake duba tsofaffin shari’o’in tsare mutane domin tabbatar da cewa ba a ci gaba da tsare marasa laifi ba.

DA DUMI-DUMI

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kanun Labarai

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img