Daga Wakiliya
Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta saki wani manomi kuma makiyayi, Nura Idris, bayan wani bincike na cikin gida ya tabbatar da cewa babu wata hujja da ke nuna yana da alaƙa da ƙungiyar Boko Haram.
Rahotanni sun ce Darakta Janar na DSS, Oluwatosin Ajayi, ne ya bayar da umarnin a sake shi tare da ba shi diyyar gaggawa ta Naira miliyan uku domin rage masa raɗaɗin abin da ya fuskanta.
An kama Nura ne a watan Yunin 2024 a Suleja, jihar Neja, bisa zargin ta’addanci, kafin daga bisani a miƙa shi ga DSS.
Majiyoyi sun bayyana cewa bayan sake nazarin shari’arsa, jami’an binciken DSS sun gano babu wata hujja da ke tabbatar da zargin da ake masa.
Baya ga diyyar kuɗi, DSS ta yi alƙawarin taimaka masa wajen farfaɗo da harkokin kiwon dabbobi domin ya ci gaba da rayuwarsa.
Rahotanni sun kuma ce hukumar na ba wa waɗanda aka wanke daga irin waɗannan zarge-zarge tallafin jinya, kula da lafiyar ƙwaƙwalwa da kuma taimakon sake komawa rayuwa.
An ce sakin Nura na daga cikin shirin DSS na sake duba tsofaffin shari’o’in tsare mutane domin tabbatar da cewa ba a ci gaba da tsare marasa laifi ba.





