Bama samun kudi yadda ake zato, ko kwanan nan akwai Dan Majalisar da ya kasa biyan kudin makarantar ƴarsa, 700k -Dan Majalisar Tarayya Chinedu Obika

Ɗan Majalisa Ya Ce Wani Abokin Aikinsa Ya Kasa Biyan Kuɗin Makarantar ‘Yarsa Na Naira 700,000

Ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazabar AMAC/Bwari a Abuja, Chinedu Obika, ya bayyana cewa kimanin watanni biyu da suka gabata wani ɗan majalisa abokin aikinsa ya kasa biyan kuɗin makarantar ‘yarsa har Naira 700,000, lamarin da ya sa shi ya taimaka ya biya.

Obika ya bayyana hakan ne yayin wata hira da aka wallafa a shirin KAA Truths, inda yake mayar da martani kan zargin da ake yi cewa ‘yan Majalisar Tarayya na karɓar kuɗaɗe masu yawa.

A cewarsa, wannan ya nuna cewa ba dukkan ‘yan majalisa ne ke cin gajiyar abin da jama’a ke kallon “wadatar kuɗi” a Majalisar Dokoki ba.

Ya kuma ce wasu ‘yan majalisar da ba sa yawan magana a zauren majalisa ba wai saboda ana ba su wani abu ba ne, illa saboda ba su da wani abin da za su nuna daga mukamansu.

Sai dai Obika bai bayyana sunan ɗan majalisar da ya ce ya taimaka wa wajen biyan kuɗin makarantar ‘yarsa ba.

Hakazalika, ya jaddada cewa dukkan haƙƙoƙi da alawus-alawus da ‘yan Majalisar Tarayya ke samu a bayyane suke, tare da ƙalubalantar ‘yan Najeriya su riƙa gabatar da hujjoji kan duk wata magana da ake yi game da albashinsu da alawus-alawus maimakon jita-jita.

DA DUMI-DUMI

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Kanun Labarai

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Shaida Mata Zai Auri Wata – Rundunar Yan Sanda

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Sanar da Ita Cewa Zai Auri Wata — Rundunar 'Yan Sanda

Mata Sun Fi Maza Cika Alƙawarin Biyan Bashi – Inji Rahoton Moniepoint

Moniepoint ta ce alkaluman sun nuna cewa, duk da matsalolin da mata ke fuskanta wajen samun rance saboda buƙatar jingina ko rashin tarihin bashi, suna daga cikin rukunin masu kasuwanci da suka fi nuna amana wajen biyan bashin da suka karɓa.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img