Barrista Hamza Nuhu Dantani ya zargi gwamnatin Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum, da take haƙƙin É—an Adam tare da amfani da jami’an tsaro wajen dakile ‘yancin faÉ—ar albarkacin baki.
Lauyan ya ce akwai mutane da dama da aka kama ko aka gurfanar a kotu ba tare da ingantattun hujjoji ba, inda ya yi ikirarin cewa wasu matasa ma an yanke musu hukuncin É—aurin shekaru biyar duk da cewa ba a tabbatar da laifinsu ba.
Ya ce daga baya Kotun Ɗaukaka Ƙara ta soke hukuncin, tare da wanke su daga dukkan zarge-zargen.
A cewarsa, mafi yawan waÉ—anda abin ya shafa matasa ne da ‘ya’yan talakawa waÉ—anda ba su da Æ™arfin É—aukar lauya domin kare kansu.
Barrista Dantani ya kuma buƙaci Gwamna Zulum da ya sasanta da duk wanda aka tauye masa haƙƙinsa tare da neman afuwa idan har an zalunce shi, yana mai cewa adalci da neman gafara alamun mutunci ne, ba rauni ba.
Ya kammala da cewa: “A Æ™arshe, hukuncin Allah shi ne mafi girma, kuma babu wanda zai tsere masa.
“Wakiliya ta lura cewa waÉ—annan zarge-zarge ra’ayi ne da ikirarin Barrista Hamza Nuhu Dantani. Gwamna Babagana Umara Zulum ko gwamnatin Jihar Borno ba su mayar da martani kan waÉ—annan zarge-zarge a cikin bayanin da aka wallafa ba.





