Daga Wakiliya
Shugaban Amurka, Donald Trump, ya ce matakan soji da ƙasarsa ta ɗauka sun taimaka wajen dakatar da kashe-kashen Kiristoci a Najeriya.
Trump ya bayyana haka ne yayin wani taro a birnin Washington, inda ya ce hare-haren da Amurka ta kai sun yi wa shugabannin masu tayar da kayar baya mummunar illa.
A cewarsa, an kashe dubban Kiristoci da suka haÉ—a da mata, yara da tsofaffi kafin matakan da Amurka ta É—auka.
Ya kuma yi ikirarin cewa an kashe jagoran ƙungiyar da mataimakansa, lamarin da ya sa sauran mayaƙan suka ja da baya saboda tsoron ƙarin hare-haren Amurka.
Sai dai Trump bai bayyana cikakken bayani kan irin harin da ya ce Amurka ta kai a Najeriya ko lokacin da hakan ya faru ba.





