Shugaban Serbia Zai Yi Murabus Bayan Zanga-Zanga Kan Mutuwar Mutum 16

Daga Wakiliya

Shugaban ƙasar Serbia, Aleksandar Vučić, ya bayyana cewa zai yi murabus cikin makonni masu zuwa, tare da ba da damar gudanar da zaɓen shugaban ƙasa da na ‘yan majalisa kafin wa’adinsu ya ƙare.

Vučić ya sanar da hakan ne yayin wani gangamin magoya bayansa a babban birnin ƙasar, Belgrade, bayan kusan watanni 18 ana gudanar da zanga-zangar adawa da gwamnatinsa ƙarƙashin jagorancin ɗalibai.

Zanga-zangar ta samo asali ne bayan rushewar rumfar tashar jirgin ƙasa a birnin Novi Sad a watan Nuwamban 2024, lamarin da ya yi sanadin mutuwar mutum 16. Masu zanga-zangar sun ce hatsarin ya nuna gazawar gwamnati wajen gudanar da ayyukan gine-gine da kuma yawaitar cin hanci da rashawa.

Ko da yake Vučić ya ce zai sauka daga kujerar shugaban ƙasa, masana na ganin hakan ba yana nufin zai fice daga siyasa ba, domin akwai yiwuwar ya sake neman kujerar Firaminista idan jam’iyyarsa ta lashe zaɓen.

A nasa bangaren, ‘yan adawa sun ce matakin da shugaban ya ɗauka na nufin ƙoƙarin dakile tasirin zanga-zangar da kuma ƙarfafa matsayin jam’iyyarsa kafin zaɓe.

DA DUMI-DUMI

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kanun Labarai

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama'a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya - CBN

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img