Daga Wakiliya
Ɗan Majalisar Wakilan Amurka, Riley Moore, ya bayyana cewa ƙasarsa za ta sa ido sosai kan yadda za a gudanar da babban zaɓen Najeriya na shekarar 2027.
Moore ya bayyana hakan ne a wata hira da ya yi da NoireTV, inda ya ce shi da gwamnatin Donald Trump za su bibiyi yadda zaɓen zai gudana da kuma ko an gudanar da shi cikin adalci.
Ya kuma ce Majalisar Dokokin Amurka na duba wasu dokoki da za su iya shafar dangantakar Amurka da Najeriya, musamman kan batun ‘yancin addini da kuma tallafin tsaro.
A cewarsa, wani kudirin kasafin kuɗi da ake tattaunawa a Majalisar ya ƙunshi sharuddan da za su iya takaita wasu nau’ikan tallafin Amurka ga Najeriya, har sai gwamnatin ƙasar ta ɗauki matakai kan hare-haren da ake kai wa a wasu sassan ƙasar da kuma batun tsaro.
Moore, wanda ke ɗaya daga cikin masu goyon bayan kudirin Nigeria Religious Freedom and Accountability Act of 2026, ya ce zai ci gaba da tattaunawa da Shugaba Trump kan lamarin, yana mai bayyana shi a matsayin muhimmin batu ga gwamnatin Amurka.





