Daga Wakiliya
Gwamnatin Amurka ta sanya sunan wani dan Najeriya, Mukhtar Adamu Muhammad, da kuma kamfanoni uku na canjin kudi da ke aiki a Najeriya cikin jerin mutanen da take zargi da taimakawa harkokin kudaɗen kungiyar ta’addanci ta ISIS.
A cewar Ma’aikatar Harkokin Wajen Amurka, an zargi Mukhtar Adamu da amfani da kamfanonin canjin kudi wajen sauƙaƙa zirga-zirgar kudaden da ake dangantawa da ISIS a Yammacin Afirka.
Kamfanonin da aka ambata sun hada da Generation Currency Bureau De Change Limited da Nine to Nine Exchange Bureau De Change Limited a Lagos, sai kuma Manhattan Bureau De Change Limited da ke Kano.
Amurka ta ce matakin wani bangare ne na kokarinta na dakile hanyoyin samun kudaden kungiyoyin ta’addanci a duniya, tare da jaddada ci gaba da hadin gwiwa da Najeriya wajen yaki da ta’addanci.
Hukumar ta bayyana cewa matakin ya shafi mutane uku da kamfanoni shida daga kasashe daban-daban, ciki har da Najeriya, Faransa, Siriya da Turkiyya.





