A Watan Yuni, Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

Kuɗin Da Ke Hannun Jama’a Ya Ragu Da Naira Biliyan 486 A Najeriya – CBN

 

Adadin kuɗin da ke hannun jama’a ba tare da an ajiye su a bankuna ba ya ragu zuwa Naira tiriliyan 4.92 a watan Yunin 2026, mafi ƙanƙanta cikin watanni bakwai, a cewar sabbin bayanan Babban Bankin Najeriya (CBN).

 

Bayanan sun nuna cewa kuɗin da ke wajen bankuna sun ragu daga Naira tiriliyan 5.41 a watan Disambar 2025 zuwa Naira tiriliyan 4.92 a watan Yunin 2026, raguwar da ta kai Naira biliyan 485.8, wato kusan kashi 9% cikin watanni shida.

 

Haka kuma, jimillar kuɗin da ke yawo a faɗin ƙasar ta ragu daga Naira tiriliyan 5.73 zuwa Naira tiriliyan 5.52 a daidai wannan lokaci.

 

Rahoton ya nuna cewa kusan kashi 89% na kuɗin da ke yawo a ƙasar har yanzu na hannun jama’a ne, yayin da sauran ke cikin tsarin bankuna.

 

CBN ya danganta wannan ci gaba da ƙoƙarinsa na ƙara yawan mutanen da ke amfani da harkokin kuɗi ta hanyar bankuna da kuma bunƙasa amfani da hanyoyin biyan kuɗi na zamani.

 

A lokacin ƙaddamar da shirin Payments System Vision 2028, Gwamnan CBN, Olayemi Cardoso, ya ce bankin na da burin kai Najeriya ga kashi 95% na financial inclusion nan da shekarar 2028, tare da rage dogaro da kuɗin hannu.

 

Cardoso ya jaddada cewa manufar CBN ita ce kuɗin hannu su daina kasancewa hanyar biyan kuɗi mafi rinjaye, yayin da ake ƙarfafa biyan kuɗi ta hanyoyin dijital domin inganta tattalin arziki da kuma ƙara amincewar masu zuba jari.

DA DUMI-DUMI

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Kanun Labarai

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 – Nentawe Yilwatda

APC Za Ta Yi Amfani da Cikakken Ƙarfinta Domin Lashe Zaɓen 2027 Daga Kan Shugaban Kasa Har Kansila - Nentawe Yilwatda

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Tsoron Talauci Na Jefa Mutane Da Dama Cikin Matsananciyar Damuwa – Masana

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa, Kimanin Naira Tiriliyan 16, Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Aliko Dangote Ya Yi Wasiyyar A Ware Kashi Ɗaya Bisa Uku Na Dukiyarsa Domin Ayyukan Jin Ƙai — Halima Dangote

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, sanye da dankwali da aka rubuta “JESUS”

Kyaftin ɗin Super Falcons, Rashidat Ajibade, na bayyana bangaskiyarta ga Yesu a duk inda ta je.

Har Tsawon Wane Lokaci Za a Iya Ajiye Kifi a Firiza Kafin Ya Lalace?

Yawan Lokacin da Kifi Zai Iya Ɗauka a Firiza Kafin Ya Lalace

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Wani Magidanci a Kano Ya Kashe Wani Mutum Saboda Ya Yi Zargin Yana Neman Matarsa – Kiyawa

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Shaida Mata Zai Auri Wata – Rundunar Yan Sanda

Budurwa Ta Yanke Gaban Saurayinta a Kano Bayan Ya Sanar da Ita Cewa Zai Auri Wata — Rundunar 'Yan Sanda
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img