2027: Ina cikin matsala, don na san idan Atiku ko Obi suka kayar da Tinubu, da ni za su fara — Wike

DA DUMI-DUMI

2027: Ina cikin matsala, don na san idan Atiku ko Obi suka kayar da Tinubu, da ni za su fara — Wike

Daga Wakiliya

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce yana ganin zai kasance mutum na farko da za a far wa idan Shugaba Bola Tinubu ya sha kaye a zaɓen shugaban ƙasa na 2027.

Wike ya bayyana haka ne yayin wata tattaunawa da manema labarai a ranar Laraba, inda ya ce yana sane da haɗarin siyasar da yake yi. Shi yasa a yanzu babban abin da ya fi mayar da hankali a kai shi ne ganin Tinubu ya sake lashe zaɓen shugaban ƙasa.

“Kowace rana idan zan kwanta, ina tunanin sake zaɓen shugaban ƙasa. Idan ina cin abinci, ina tunanin sake zaɓensa. Duk abin da nake yi yanzu ya shafi sake zaɓen shugaban ƙasa ne.” – a cewar ministan

- Advertisement -spot_img

Leave a Reply

- Advertisement -spot_img
Za ku so wadannan

Gwamnatin Najeriya za ta fara biyan tsoffin ma’aikatan Nigeria Airways Naira biliyan 18

Sai dai ya bayyana cewa gwamnati za ta biya kuɗin da aka tantance kuma aka tabbatar da shi, ba tare da ƙarin kuɗin da ya dace da hauhawar farashi na tsawon shekaru 20 ba.
- Advertisement -spot_img

Labarai masu alaka

- Advertisement -spot_img