Hisbah ta lashi takobin ƙara kaimi wajen yaƙi da ’yan daudu a Kano

DA DUMI-DUMI

Hisbah ta lashi takobin ƙara kaimi wajen yaƙi da ’yan daudu a Kano

Daga Wakiliya

Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta ce za ta ƙara kaimi wajen yaƙi da ayyukan da take bayyana a matsayin rashin ɗa’a, bayan kama wasu mutane 22 da ake zargi da yin kwaikwayon halayen jinsi daban da nasu (daudu).

Mataimakin Babban Kwamandan Hukumar Hisbah, Dr Mujahid Aminuddeen, ya tabbatar da kamen, yana mai cewa an kama mutanen ne a wasu sassan birnin Kano, ciki har da Zoo Road da Court Road da kewaye.

Ya ce yawancin waɗanda aka kama sun shigo Kano ne daga wasu jihohin Najeriya.

A cewarsa, waɗanda aka kama sun ƙunshi mata 10 da maza 12, kuma wasu daga cikinsu sun amsa cewa suna gudanar da ayyukan kawalci wato “hook-up”, tare da yin amfani da miyagun ƙwayoyi.

Ya kuma jaddada cewa Hisbah ba za ta lamunci ayyukan da take ganin sun saɓa wa ɗabi’a da dokokin jihar ba, yana mai cewa hukumar za ta ƙara tsaurara matakan dakile irin waɗannan ayyuka a Kano.

- Advertisement -spot_img

Leave a Reply

- Advertisement -spot_img
Za ku so wadannan

Gwamnatin Najeriya za ta fara biyan tsoffin ma’aikatan Nigeria Airways Naira biliyan 18

Sai dai ya bayyana cewa gwamnati za ta biya kuɗin da aka tantance kuma aka tabbatar da shi, ba tare da ƙarin kuɗin da ya dace da hauhawar farashi na tsawon shekaru 20 ba.
- Advertisement -spot_img

Labarai masu alaka

- Advertisement -spot_img