Daga Wakiliya
An samu tsaiko a aikin kwaso wasu ‘yan Najeriya 271 daga Afirka ta Kudu bayan an gano tsagewa a gilashin gaban É—akin matuÆ™an jirgin (cockpit), lamarin da ya hana jirgin tashi daga birnin Johannesburg.
Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Najeriya, Kimiebi Imomotimi Ebienfa, ya ce an dakatar da tashin jirgin ne domin tabbatar da tsaron fasinjoji, yana mai cewa kamfanin Air Peace ya shirya tura wani jirgi domin ci gaba da aikin kwaso mutanen.
Ebienfa ya bayyana cewa an shirya jirgin ne domin dawo da ‘yan Najeriya 271, amma aka gano matsalar ne kafin tashinsa.
Ya kuma nemi afuwar waÉ—anda abin ya shafa, yana mai tabbatar da cewa za a tura wani jirgi cikin gaggawa domin kammala aikin.
Tun bayan sabbin hare-haren da ake kai wa baÆ™in haure a Afirka ta Kudu, gwamnatin tarayya ta ce ta riga ta kwaso ‘yan Najeriya 859 zuwa gida lafiya.





