Daga Wakiliya
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya musanta zargin da Hukumar Yaƙi da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta yi masa na cewa ya karya umarnin kotu tare da amfani da damar zuwa jinya ba bisa ƙa’ida ba.
A wata sanarwa da mai ba shi shawara kan yaɗa labarai, Muyiwa Adekeye, ya fitar a ranar Laraba, El-Rufai ya ce sanarwar da ICPC ta fitar ranar 7 ga Yuli ta ƙunshi bayanan da ba su dace da gaskiya ko doka ba.
Sanarwar ta ce rashin halartar El-Rufai zaman kotu ya samo asali ne daga matsalar rashin lafiya da aka sanar da ICPC tun kafin zaman kotun, tare da zargin cewa an hana likitansa na kashin kansa, Farfesa Bello Abubakar, damar duba lafiyarsa.
El-Rufai ya ce buƙatar kai shi Asibitin Ƙasa da ke Abuja domin duba lafiyarsa ta riga ta kasance kafin sanar da shi ranar zaman kotu, kuma hakan ya yi daidai da umarnin kotu da ya ba shi damar samun kulawar lafiya.
Ya kuma musanta cewa ya karya wani umarnin kotu yayin da yake asibiti, yana mai cewa babu wani umarni da ya hana mutane ziyartar sa yayin jinya.
Haka kuma, ya nemi ICPC ta bayyana dalilin kama Farfesa Bello Abubakar tare da sakin sa ba tare da wani sharaɗi ba idan ba ta da hujjojin zargin da take masa.
A ƙarshe, El-Rufai ya buƙaci ICPC ta janye sanarwar da ta fitar tana zarginsa da karya umarnin kotu, yana mai jaddada cewa zai ci gaba da kare haƙƙinsa na samun shari’a ta adalci da kuma kulawar lafiya bisa tanadin doka.





