Daga Wakiliya
Kwamishinan ‘Yan Sandan Babban Birnin Tarayya (FCT), Ahmed Sanusi, ya gargadi jami’an ‘yan sanda da su daina karɓar rashawa da kuma kwace kuɗi daga masu ababen hawa yayin gudanar da aikinsu.
Sanusi ya yi wannan gargaɗi ne a ranar Asabar yayin wani taron tsaro da aka gudanar domin duba yadda ake gudanar da ayyukan tsaro da kula da zirga-zirga a Abuja.
Ya ce rundunar ba za ta ƙara kare jami’an da ke cin zarafin direbobin Keke Napep da masu motoci ta hanyar karɓar kuɗi ba bisa ƙa’ida ba.
A cewarsa, koke-koken da jama’a ke yi kan cin zarafin jami’an ‘yan sanda sun yi yawa, don haka rundunar ta shirya tsabtace cikinta tare da hukunta duk masu hannu a irin waɗannan ayyuka.
“Ba ma son jin wani rahoto cewa ana karɓar kuɗi daga direbobin Keke Napep ko masu motoci a Abuja. Idan aka kama ka da hakan, kai ɓarawo ne.
“Ba za ka iya zama ɗan sanda kuma ɓarawo a lokaci guda ba. Dole ne ka zaɓi ɗaya,” in ji Sanusi.





