Matar El-Rufai ta zargi gwamnatin Tinubu da yi wa El-Rufai bita da ƙullin siyasa

DA DUMI-DUMI

Matar El-Rufai ta zargi gwamnatin Tinubu da yi wa El-Rufai bita da ƙullin siyasa

Daga Wakiliya

Matar tsohon gwamnan Kaduna, Asia El-Rufai, ta zargi gwamnatin tarayya a ƙarƙashin Shugaba Tinubu da tsare mijinta na dogon lokaci da kuma gudanar da bincike a kansa bisa dalilan siyasa.

Asia, wadda lauya ce, ta bayyana hakan a cikin wani shirin bidiyo da ƙungiyar Justice For El-Rufai Project ta fitar.

Ta ce ba a zargi mijinta da wani laifi ba a lokacin da yake cikin jam’iyyar APC, sai dai an fara yi masa zarge-zarge da barazana ne biyan ficewarsa daga jam’iyyar APC zuwa SDP zuwa ADC.

Asia ta kuma ce El-Rufai ya musanta dukkan zarge-zargen da ake yi masa a gaban kotuna uku, tare da neman beli.

Ta ce laifukan da ake tuhumarsa da su na da damar beli, tana mai cewa: “Beli hakki ne, ba gata ba.”

Don haka suna ɗaukar tsare tsohon gwamnan a matsayin bita da ƙullin siyasa.

- Advertisement -spot_img

Leave a Reply

- Advertisement -spot_img
Za ku so wadannan

Gwamnonin APC Ba Su Ji Daɗi Da Na Zama Ministan Abuja Ba – Muƙamina ya tsokane masu ido -Wike

Ya ƙara da cewa kasancewar mutum gwamna ba ya nufin duk abin da ya yanke dole ne ya faru ba, yana mai cewa shi ma ya taɓa kayar da ɗan takarar gwamnan da ke kan mulki a zaɓen 2015, a lokacin da yake Ministan Ƙasa.
- Advertisement -spot_img

Labarai masu alaka

- Advertisement -spot_img