Gwamnonin APC Ba Su Ji Daɗi Da Na Zama Ministan Abuja Ba – Muƙamina ya tsokane masu ido -Wike

DA DUMI-DUMI

Gwamnonin APC Ba Su Ji Daɗi Da Na Zama Ministan Abuja Ba – Muƙamina ya tsokane masu ido -Wike

 

Daga Wakiliya

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya zargi gwamnonin jam’iyyar APC da rashin jin daɗin kasancewarsa Ministan Babban Birnin Tarayyar Abuja, FCT.

Wike ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi ranar Talata, yayin da yake magana kan adawar da wasu gwamnonin APC ke yi wa haɗin gwiwar Rainbow Coalition a Jihar Rivers.

Ministan ya kuma zargi gwamnonin APC da yaudarar Gwamna Siminalayi Fubara a lokacin rikicin siyasar jihar, yana mai cewa sun kasa tabbatar masa da wa’adi na biyu.

“Ba su ji daɗin cewa an ba ni Ministan FCT ba,” in ji Wike.

Ya ƙara da cewa kasancewar mutum gwamna ba ya nufin duk abin da ya yanke dole ne ya faru ba, yana mai cewa shi ma ya taɓa kayar da ɗan takarar gwamnan da ke kan mulki a zaɓen 2015, a lokacin da yake Ministan Ƙasa.

- Advertisement -spot_img

Leave a Reply

- Advertisement -spot_img
Za ku so wadannan

Shaharata a ƙauyukan Gombe ta fi abin da ake gani a kafafen sada zumunta’ – Pantami

Ya ce idan aka zaɓe shi, gwamnatinsa za ta fi mayar da hankali kan bunƙasa ilimi, samar da ayyukan yi da koyar da matasa sana’o’in zamani, maimakon dogaro da rabon kuɗi.
- Advertisement -spot_img

Labarai masu alaka

- Advertisement -spot_img