Zan so na rika fitowa a budurwa maimakon uwa a fim -in ji Rahama Sidi
Daga Wakiliya
Fitacciyar jarumar Kannywood, Rahama Sidi Aliyu, ta ce tana son ta rika fitowa a matsayin budurwa a fina-finai maimakon matsayin uwa, saboda a cewarta ba ta kai shekarun da za a rika saka ta a irin wannan matsayi ba.
Rahama Sidi ta bayyana hakan ne yayin wata hira da tashar Fact News, inda ta ce ta kwashe kusan shekara takwas tana harkar fim, kuma fim din farko da ta fara yi shi ne Farar Mace na Abubakar Dan Sudan.
Jarumar ta ce daga cikin fina-finan da ba za ta taba mantawa da su ba akwai fim din Labari na, wanda ta bayyana cewa yana da muhimmanci a rayuwarta ta sana’ar fim.
Ta kuma yi magana kan wata matsala da ta taba fuskanta bayan wata hira da ta yi da BBC, inda ta ce an samu rashin fahimta bayan ta bayyana cewa iyayenta ‘yan Ghana ne. Ta ce ba haka lamarin yake ba, domin asalinsu ‘yan Kano ne, sai dai fatauci ya kai su Ghana.
Rahama Sidi ta ce harkar fim ta taimaka mata wajen cimma wasu nasarori a rayuwa, ciki har da mallakar mota da gida nata, tare da wasu abubuwa da dama da ta samu ta hanyar sana’ar.
Ta musanta jita-jitar cewa ta taba auren wani dan fim, inda ta ce abin da ya faru shi ne ta auri dan wani fitaccen jarumi ne, Kasimu Yaro.
Jarumar ta ce babban burinta a gaba shi ne ta zama babbar furodusa a masana’antar shirya fina-finai.




