Daga Wakiliya
Wani mutum Aliyu Nuhu ya ba da labarin abin da ya ce ya faru da shi yayin da yake tafiya daga Fatakwal zuwa Onitsha.
A cewarsa, da ya isa Owerri, wani jami'in Hukumar Kiyaye Haɗurra ta Kasa (FRSC) ya tsayar da shi, yana zarginsa da rashin sanya bel ɗin kujera (seatbelt).
Direban (Aliyu) ya ce ya roƙi jami'in da ya yi masa afuwa, yana mai alƙawarin cewa ba zai sake maimaita kuskuren ba, amma jami'in ya ƙi.
Ya ƙara da cewa jami'in ya yi barazanar ƙwace lasisin tuƙinsa tare da kai motarsa ofishin FRSC. Bayan doguwar roƙo, direban ya ce jami'in ya karɓi N30,000, wanda ya ce shi ne kaɗai kuɗin da ya rage masa domin sayen man fetur da sauran buƙatun tafiyarsa.
A cewarsa, bayan ya ci gaba da tafiya, yana dab da shiga Onitsha sai wayar da ke gefensa ta fara ƙara. Da ya duba, sai ya ga Samsung Galaxy S24, kuma bayan ya ɗaga kiran, ya gano cewa wayar ta jami'in FRSC ce da ya manta a cikin motarsa.
Yanzu, a cewar direban, jami'in yana ta roƙonsa da ya dawo masa da wayar.
Idan kai ne a irin wannan hali, me za ka yi?




