Halima tsohuwar matar Bashir El-Rufai ta yi magana kan rayuwarta bayan rabuwar aurensu
Daga Wakiliya
Halima Nwakego, tsohuwar matar Bashir El-Rufai, ta yi magana kan rayuwarta bayan rabuwar aurensu, da yadda take renon ’ya’yanta tagwaye.
Bashir, ɗan tsohon gwamnan Kaduna Nasir El-Rufai, ya auri Halima, ’yar tsohon Sanatan Jigawa Ibrahim Kazaure, a shekarar 2020.
Sun haifi ’ya’ya tagwaye maza biyu a shekarar 2021.
A watan Yulin 2024 ne aurensu ya ƙare.
Bashir ya sanar da rabuwar a lokacin, inda ya yi amfani da kalmar “Gen Z wahala”. Daga baya ya nemi afuwa kan yadda ya sanar da batun.
A wani rubutu da ta wallafa, Halima ta ce tun kafin ta yi aure ba ta da cikakken yakinin cewa aurenta zai daɗe.
Ta ce har tana ganin kamar aurenta zai ƙare tun kafin ya fara.
“Na shiga aure ne ina tunanin yadda zai ƙare,” in ji ta.
Halima ta ce bayan rabuwar, ta sake soyayya da wani mutum, amma dangantakar ta ƙare da ɓacin rai.
Ta ce duk da cewa ba ta da cikakken amincewa da maza, tana da babban imani da soyayya.
“Ga wanda ba shi da cikakken imani da maza kamar ni, ina da matuƙar imani da soyayya,” in ji ta.
Halima ta kuma yi magana kan rayuwarta a matsayin uwa mai renon ’ya’ya ita kaɗai, kasuwancinta da kuma rayuwa da ADHD, wato matsalar rashin iya mai da hankali na dogon lokaci.





