Tinubu ya bai wa Famadewa ragamar tsara sabon tsarin tsaron Najeriya na shekaru biyar – abin da ya sake jawo tambayar ‘wanene Oga?’ tsakaninsa da NSA Nuhu Ribadu
Daga Wakiliya
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bai wa sabon mai ba shi shawara kan harkokin tsaron cikin gida, Manjo Janar Adeyinka A. Famadewa, ragamar jagorantar aikin tsara sabon tsarin tsaron Najeriya na shekaru biyar.
Wannan mataki ya sake jawo tambayar da aka dade ana yi tun bayan naɗin Famadewa kan yadda aikinsa zai kasance a ƙarƙashin Mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu – musamman kan batun wanda ke da babban iko ko jagoranci a wasu harkokin tsaro.
A sabon tsarin da Shugaba Tinubu ya amince da shi, an ɗora wa Famadewa alhakin daidaita aikin da kuma samar da sakatariyar kwamitin da zai tsara cikakken binciken barazanar tsaro na ƙasa da kuma shirin ayyukan tsaro na shekaru biyar.
Mambobi: An kafa kwamitin ne da manyan jami’an tsaro da suka haɗa da Nuhu Ribadu, Ministan Tsaro Janar Christopher Musa, Karamin Ministan Tsaro Bello Muhammad Matawalle, Shugaban Hafsan Tsaro Janar Olufemi Oluyede, da shugabannin rundunonin soji.
Sauran mambobin sun haɗa da Shugaban Rundunar Ƙasa Laftanar Janar Waidi Shaibu, Shugaban Rundunar Sojin Sama Air Marshal Sunday Kelvin Aneke, Shugaban Rundunar Sojin Ruwa Vice Admiral Idi Abbas, Darakta-Janar na DSS Tosin Ajayi, da Darakta-Janar na NIA Ambasada Mohammed Mohammed.
Sabon tsarin zai ƙunshi National Threat Assessment, wato cikakken binciken manyan barazanar tsaron Najeriya, da kuma hanyoyin magance su na shekaru biyar.
Shugaba Tinubu ya ce manufar shirin ita ce samar da tsarin bai ɗaya da zai taimaka wa hukumomin tsaro wajen gano barazanar ƙasa, tsara abubuwan da suka fi muhimmanci da kuma daidaita yadda ake amfani da sojoji da sauran jami’an tsaro.
Ya ce ko da yake ayyukan tsaro na baya-bayan nan sun samu wasu nasarori, har yanzu akwai bukatar ƙara haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro.
Shugaban ya ba kwamitin kwanaki 90 domin kammala aikin da gabatar da shi gare shi domin amincewa.
Sai dai sanarwar ba ta ce Famadewa ya zama sama da Nuhu Ribadu a tsarin shugabancin harkokin tsaron ƙasa ba. Abin da ta bayyana shi ne cewa Famadewa ne aka ba alhakin daidaita wannan takamaiman aikin, yayin da Nuhu Ribadu yake cikin mambobin kwamitin.
Saboda haka, matakin ya sake mayar da hankali kan yadda za a raba ayyuka da iko tsakanin ofishin NSA da sabon ofishin mai ba Shugaban Ƙasa shawara kan harkokin tsaron cikin gida.





