Wani matashi a birnin New York na Amurka ya wallafa wani bidiyo a TikTok yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa aiki, inda ya tagging din Shugaban Birnin (magajin birnin New York din), Zohran Mamdani, tare da neman a gyara manyan ramukan da ke wata hanya.
Abun mamaki ko da ya dawo daga aiki daga baya a wannan rana, sai ya tarar an cike ramukan. Inda ya yi Bidiyo kuma bidiyon ya bazu sosai a shafukan sada zumunta.
Na ci karo da bidiyon ne a TikTok, amma abin da ya fi bani dariya shi ne yadda wasu ’yan Afirka, musamman ’yan Najeriya, suka mayar da martani.
Wani ya ce: “Da a Najeriya wannan abu ya faru, da kama shi za a yi.”
Wani kuma ya ce: “Da a Najeriya wani Data Boy zai taso shi gaba da zagi, ya zarge shi da bata wa kasar suna.”
Wani dan Uganda kuwa ya ce: “Da a Uganda wannan ya faru, da gwamnatin tarayya ta kafa kwamiti domin binciken ramukan. Kudin zaman kwamitin da alawus dinsa kuwa da ya fi kudin cike ramukan.”
Amma bayan barkwancin, akwai darasi mai muhimmanci a ciki.
Ya kamata ’yan kasa su iya nuna matsalolin da ke cikin al’ummominsu ba tare da tsoron a hukunta su ba. Haka kuma, ya kamata gwamnati ta dauki irin wadannan korafe-korafe a matsayin bayanan da za su taimaka wajen gyara matsaloli, ba wai ta kalli abun a matsayin kai mata hari ne ko kokarin bata mata suna ba.
— Fassarar Sharhin Ameer Lukman




