Shin Arewa na tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin samun zaman lafiya da ci gaba?
Shin Arewa tana tunanin za ta bar ’ya’yanta da mata suna yawo a kan tituna cikin talauci da rashin gata, sannan ta yi tsammanin zaman lafiya zai ci gaba? A’a, ba haka abin yake ba
Daga Zainab Isa Hayatudeen
Yayin da wasu daga cikin ’ya’yanmu suke zuwa ƙasashen waje domin karatu, akwai yaran da ba su samu ko ilimin zamani ko na addini ba. Wasu daga cikinsu kuwa rayuwarsu ta ta’allaka ne kan bara da yawo a tituna.
Za mu iya cewa batun Almajirai matsalar iyaye ce, mu ce ba ruwanmu. Amma gaskiya ita ce, wannan matsala ce da ta shafi al’umma baki ɗaya.
Shin ba mu san cewa Allah Ya haramta zalunci ba? Ko kuma mun manta da Alƙur’ani, sai dai mu ajiye shi a kan drowa (shelf) domin ado?
Mun yi tunanin za mu ci gaba da rayuwa cikin jin daɗi da almubazzaranci, yayin da wasu daga cikin mutanenmu suke fama da yunwa, har Naira dubu ɗaya kawai ta zama musu babbar matsala.
To, ina adalcin talaka? Ina hakkinsa?
Wataƙila wannan lokaci ya daɗe yana zuwa, kuma yanzu sakamakon abubuwan da muka aikata yana dawowa gare mu.
Allah Ya sa mu farka daga wannan barcin gafala. Ya sa mu tuba daga munafunci, son zuciya, kwaɗayi da jahilci. Ya sa mu gyara al’ummarmu kafin lokaci ya kure.
Amin ya Rabbal Alamin.




