Nazari: Yadda rashin tsaro ke kara jefa yaran Arewa cikin matsalar rashin zuwa makaranta
Daga Wakiliya
Rashin tsaro na kara jefa dubban yara a arewacin Najeriya cikin hadarin daina zuwa makaranta, yayin da hare-haren ‘yan bindiga da kungiyoyin ta'addanci ke tilasta rufe makarantu da kaura daga al'ummomi.
Masana ilimi da tsaro sun ce matsalar ba ta tsaya kan rasa darussa kawai ba.
Dr Obini Onuchukwu, shugaban Conference of Polytechnics and Colleges of Technology in Nigeria, ya ce dogon lokaci ba tare da zuwa makaranta ba na iya lalata tsarin karatun yara da kuma rage damar samun sakamakon ilimi mai kyau.
Ya ce yara ba sa iya cike gibin dogon rashin zuwa makaranta ta hanyar karatu a gida kawai, musamman idan ba su da kayan karatu da kulawar da ta dace.
Malamar ilimi Eloho Arhogho-Okeren ta ce wasu yara da suka bar makaranta na wani lokaci ba sa komawa, inda wasu ke shiga sana'o'in hannu, noma ko tallace-tallace.
Ta yi kira da a samar da darussan rediyo, cibiyoyin karatu ga al'umma, abinci a makaranta da shirye-shiryen dawo da yaran da suka rasa karatu.
Farfesa Al Chukwuma Okoli, masani kan harkokin tsaro, ya ce matsalar na iya kara yawan yaran da ba sa zuwa makaranta a Najeriya.
Ya ce yara da suka rasa ilimin farko na karatu da rubutu da lissafi na iya fuskantar matsaloli wajen samun aikin yi a nan gaba.
Ya kuma yi gargadin cewa yaran da ba sa makaranta na iya zama masu saukin fadawa hannun kungiyoyin ‘yan ta'adda, ‘yan bindiga da sauran kungiyoyin aikata laifuka.
A cewarsa, kare makarantu daga hare-hare ya kamata ya zama wani bangare na dabarun yaki da rashin tsaro.





