A shekara Biyun farko da hawan Tinubu mulki an kashe akalla mutane sama da 10,000 a jihohi bakwai – Amnesty
Daga Wakiliya
Ƙungiyar Amnesty International ta ce a cikin shekaru biyu na farko na gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu, aƙalla mutane 10,217 ne aka kashe a hare-haren ’yan bindiga a jihohin Benue, Niger, Katsina, Kebbi, Plateau, Sokoto da Zamfara.
A cewar ƙungiyar, jihar Benue ce ta fi yawan adadin waɗanda aka kashe, sai jihar Plateau wadda aka kashe mutane 2,630.
Amnesty ta ce yanzu fiye da shekaru uku kenan da Shugaba Tinubu ya hau mulki da alkawarin inganta tsaro, amma matsalar tsaron ƙasar ta ƙara tsananta.
Ƙungiyar ta zargi hukumomin Najeriya da gazawa wajen kare haƙƙin rayuwa, lafiyar jiki, ’yanci da tsaron dubban mutane a sassan ƙasar.
Ta kuma ce a cikin shekaru biyu na farko na gwamnatin Tinubu, wasu sabbin ƙungiyoyin masu ɗauke da makamai sun bayyana, ciki har da Lakurawa a jihohin Sokoto da Kebbi, da kuma Mamuda a jihar Kwara.
Amnesty ta ƙara da cewa ɗaruruwan ƙauyuka sun fuskanci hare-hare tare da tilasta wa mazauna barin gidajensu a jihohin Benue, Borno, Katsina, Sokoto, Plateau da Zamfara.
Ƙarin matsin rayuwa ga waɗanda suka rasa matsugunansu
Ƙungiyar ta ce yawaitar hare-haren na ƙara jefa ƙasar cikin barazanar fuskantar matsalar jinƙai.
A cewar Amnesty International, yawancin mutanen da suka rasa matsugunansu a jihohin Plateau da Katsina sun shaida mata cewa dole sai sun nemi taimakon jama'a domin samun abin da za su ci da gudanar da rayuwarsu ta yau da kullum.
A gundumar Dangulbi da ke jihar Zamfara kuma, manoma na kallon amfanin gonarsu, musamman dankalin Hausa, yana lalacewa saboda ’yan bindiga sun hana su kai kayan amfanin gonar kasuwa mafi kusa.
Amnesty ta ce a ƙarƙashin dokokin ƙasa da ƙasa na kare haƙƙin ɗan Adam, hukumomi na da alhakin kare rayukan jama'a da kuma tabbatar da cewa an hukunta waɗanda ake zargi da hannu a kashe-kashen.
Ta ce hukumomin Najeriya suna kuma da alhakin tabbatar da cewa waɗanda hare-haren suka shafa sun samu damar neman adalci da kuma diyya ko wasu hanyoyin magance matsalolin da suka fuskanta.
Ƙungiyar Amnesty International Nigeria ce ta wallafa bayanan.




