DG Abdul’Aziz Murna Ta Koma Ciki: Tinubu ya janye sunayen kwamitin yakin neman zaɓensa na 2027 da APC ta fitar ya sa a sake gyare-gyare
Daga Wakiliya
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya bayar da umarnin sake duba tare da gyara jerin sunayen kwamitin yakin neman zaɓen jam’iyyar APC na zaɓen shugaban ƙasa na 2027.
Rahotanni sun ce matakin ya biyo bayan koke-koken wasu manyan jiga-jigan jam’iyyar da suka nuna cewa jerin farko bai yi la’akari da wasu muhimman shugabanni da kuma tsarin rabon mukamai tsakanin yankuna ba.
An ce Shugaba Tinubu ya umarci ofishin Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, tare da shugabannin Majalisar Ƙasa da Kwamitin Zartarwa na Ƙasa na APC, da su sake tsara jerin sunayen.
A jerin farko, tsohon gwamnan Zamfara, Sanata Abdul’aziz Yari, ne aka nada Darakta-Janar na kwamitin.
Sai dai rashin sanya sunan Mataimakin Kakakin Majalisar Wakilai, Benjamin Kalu, ya jawo suka, musamman daga wasu masu ruwa da tsaki a Kudu maso Gabas.
Haka kuma, yadda aka tsara mukaman shugabannin Majalisar Ƙasa ya haifar da ce-ce-ku-ce, inda aka sanya Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, a matsayin Mataimakin Darakta-Janar na bangaren yakin neman zaɓen Kudu.
Wasu daga cikin jiga-jigan APC sun ce ya kamata a bai wa Akpabio matsayi da ya dace da matsayinsa na Shugaban Majalisar Dattawa, bisa tsarin shugabanci na ƙasa.
Rahotanni sun kuma ce jerin farko bai ƙunshi wasu daga cikin fitattun ‘yan jam’iyyar da suka taka muhimmiyar rawa a yakin neman zaɓen APC na 2023 ba.
Daga cikinsu akwai tsohon Darakta-Janar na kwamitin yakin neman zaɓen 2023, Simon Lalong; Ministan Jiragen Sama da Sararin Samaniya, Festus Keyamo; mai ba shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, Nuhu Ribadu; da tsohon Gwamnan Kogi, Yahaya Bello.
Haka kuma, tsoffin gwamnoni Gbenga Daniel da Ibikunle Amosun, da tsohon ɗan takarar gwamnan Edo, Osagie Ize-Iyamu, ba su cikin jerin.
Rahotanni sun ce rashin sanya sunan Gwamnan Edo, Monday Okpebholo, shi ma ya jawo damuwa saboda muhimmancin gwamnoni wajen tattara magoya bayan jam’iyya a jihohinsu.
Sai dai babu wata alama da ke nuna cewa Shugaba Tinubu ya sauya matsayinsa kan nadin Abdul’aziz Yari a matsayin Darakta-Janar.
A yayin da ake sake tsara kwamitin, Shugaba Tinubu ya bukaci waɗanda aka ambata a jerin farko da su fara aikin ƙarfafa jam’iyya da wayar da kan jama’a kan nasarorin gwamnatinsa da sauye-sauyen tattalin arziki.
Ya ce APC na da nasarorin da za ta gabatar wa al’umma yayin da zaɓen 2027 ke ƙara matsowa.
Yanzu dai ana sa ran sabon jerin kwamitin zai ƙara wakiltar sassa daban-daban na jam’iyyar tare da shigar da manyan jiga-jiganta kafin fara babban yaƙin neman zaɓen 2027.




