Ya Allah Ka Kare Mu Daga Mazan Azzalumai — Labarin Matar Da Ta Haihu Ba Tare Da Tallafin Ko Tsinke Daga Mijinta Ba Ya Girgiza Zuciya
Ta haihu babu ko tsinke na haiuwa daga mijin, ya ki rako ta Asibiti, babu wani nashi kuma ko sisi bai bayar ba, ita ce matar shi ta huɗu, haihuwa na 11, yan uwanta suke komai, tana cikin nakuda ma sai da tayi mashi tuwo kafin ta taho Asibiti….
Daga Wakiliya
“Ina zaune a wajen nan (Asibiti) naga abun mamaki, wasu mata ne su biyu da Attendant daga labour room (dakin haihuwa) a asibitin Teaching Hospital inda muka fi sani da Nursing Home nan Kaduna.
Sisters din su ce suka kawo Asibiti Rai a hannun Allah za ta haihu, cikin hukuncin Ubangiji ta haihu ta sauka lafiya,Amma babu komai na haihu, Ina mijin yake ya rantse da Allah ba zai zo ba, ya bada kuɗi ne da za su zo? a a ko sisi bai bayar ba.
Yanzu 23k suke nema babu, kuma ba zai zo ba, babu wani nashi, ita ce matar shi ta huɗu, haihuwa na 11, yan uwanta suke komai,tana cikin nakuda ma sai da tayi mashi tuwo kafin ta taho.
Wait Are some people human being at all
For God's sake ta yaya zaki zauna kina haihuwa yan uwanki ne za su dinga kula dake, baki da hankali ne, ke wacce irin sakarya ce.
For him I will not say anything Amma wallahi duk wanda yayi da kyau ya sani.
Ya Allah kayi mana kariya, kayi mana katanga karfe da Azzalumai maza, marasa mutunci, mugaye.
Ya Allah ka bamu ikon cin jarabawar mu
Labari daga Nanaah Ismaeel Kaduna




