Da Tinubu ya so APC ta ci zaɓen Osun ko ta halin ƙa-ƙa, da ni za a tura jihar -Wike

Da Tinubu ya so APC ta ci zaɓen Osun ko ta halin ƙa-ƙa, da ni za a tura jihar

Daga Wakiliya

Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya ce da Shugaba Bola Tinubu na son jam’iyyar APC ta lashe zaben gwamnan Osun ko ta halin-ƙa-ƙa, da ya je jihar domin taimaka mata ta samu nasara.

Wike ya bayyana hakan ne ranar Talata yayin da yake magana da ’yan jarida a Abuja, bayan duba wasu wuraren da ambaliyar ruwa ta ci a Maitama.

Da yake magana kan sakamakon zaben da Gwamna Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP ya lashe, Wike ya ce APC za ta iya samun nasara idan Shugaba Tinubu ya kuduri aniyar ganin ta yi nasara ko ta halin kaka.

Ya ce: “Da Shugaban kasa na son cin zaben Osun da ko-ta-halin ƙa-ƙa, da na je can, kuma da mun ci zaben. Babu abin da gwamnan zai iya yi.”

Nyesom Wike, wanda tsohon gwamnan Jihar Rivers ne, ya kasance cikin ’yan PDP da ke goyon bayan Bola Tinubu tun bayan zaben shugaban kasa na 2023, duk da cewa har yanzu yana cikin jam’iyyar PDP.

An nada Wike Ministan Abuja a gwamnatin Bola Tinubu, wadda jam’iyyar APC ke jagoranta.

DA DUMI-DUMI

APC ta zargi an yi mata magudin zaɓe a Osun, ta nemi a sake duba sakamakon

Sai dai APC ta ce tana ci gaba da duba sakamakon da yadda aka gudanar da zaɓen, wanda zai iya zama matakin farko na ƙalubalantar sakamakon da aka sanar.

Wike ya umarci a rushe duk gidajen da suka toshe hanyoyin ruwa a Abuja

Wike ya umarci rushe gidajen da aka gina kan hanyoyin ruwa a Abuja Daga Wakiliya  Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya umarci hukumomin birnin da su fara rushe gidajen da aka gina ko kuma suka tare hanyoyin ruwa a Abuja. Wike ya bayar da umarnin ne bayan ya duba wuraren da ambaliyar ruwa ta shafa a Maitama ranar Talata. Ya ce za a fara aikin nan take kuma za ayi ta aikin har zuwa ranar Asabar, ba tare da la'akari da masu gidajen ba. Ministan ya ce wasu daga cikin gine-ginen mallakin 'yan majalisa da wasu masu hannu da shuni ne, amma doka za ta shafi kowa. Ya ce gine-gine a kan hanyoyin ruwa, toshe magudanan ruwa da zubar da shara na daga cikin abubuwan da ke haddasa ambaliyar ruwa a Abuja. Wike ya kuma umarci hukumomin FCT da su gaggauta kwashe laka da datti daga magudanan ruwa a babban birnin,  Ya ce sauyin yanayi da yawan ruwan sama na taka rawa wajen ambaliyar, amma ayyukan mutane ma na kara tsananta matsalar. Ministan ya ce ba za a dakatar da rushe-rushen saboda ana cikin lokacin siyasa ba, yana mai cewa gwamnati na da niyyar tabbatar da dokokin tsara birnin.

Daga yanzu ‘Daukar doka a hannu’ daidai yake da kisan kai — IGP Disu ya gargadi ’yan Najeriya

Ya gargadi mutanen da ke shirya ko tunzura jama'a, wadanda ke daukar hotuna ko bidiyon abin da ke faruwa su yada shi, da kuma wadanda ke hana ’yan sanda shiga tsakani ko kai agajin gaggawa kan wanda ake zargi, cewa su ma za su iya fuskantar tuhuma.

Ya Allah Ka Kare Mu Daga Maza Azzalumai – labarin wata maijego da na gani a asibiti ya girgiza ni

Ta haihu babu ko tsinke na haiuwa daga mijin, ya ki rako ta Asibiti, babu wani nashi kuma ko sisi bai bayar ba, ita ce matar shi ta huɗu, haihuwa na 11, yan uwanta suke komai, tana cikin nakuda ma sai da tayi mashi tuwo kafin ta taho Asibiti....

Fitaccen Jarumin Fim Nicolas Cage Ya Ce Yana Iya Tuna Abin da Ya Faru Tun Yana Cikin Mahaifiyarsa

Masana kimiyya sun ce yawancin mutane ba sa iya tuna abubuwan da suka faru kafin su kai kusan shekara biyu ko uku

Kanun Labarai

APC ta zargi an yi mata magudin zaɓe a Osun, ta nemi a sake duba sakamakon

Sai dai APC ta ce tana ci gaba da duba sakamakon da yadda aka gudanar da zaɓen, wanda zai iya zama matakin farko na ƙalubalantar sakamakon da aka sanar.

Wike ya umarci a rushe duk gidajen da suka toshe hanyoyin ruwa a Abuja

Wike ya umarci rushe gidajen da aka gina kan hanyoyin ruwa a Abuja Daga Wakiliya  Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya umarci hukumomin birnin da su fara rushe gidajen da aka gina ko kuma suka tare hanyoyin ruwa a Abuja. Wike ya bayar da umarnin ne bayan ya duba wuraren da ambaliyar ruwa ta shafa a Maitama ranar Talata. Ya ce za a fara aikin nan take kuma za ayi ta aikin har zuwa ranar Asabar, ba tare da la'akari da masu gidajen ba. Ministan ya ce wasu daga cikin gine-ginen mallakin 'yan majalisa da wasu masu hannu da shuni ne, amma doka za ta shafi kowa. Ya ce gine-gine a kan hanyoyin ruwa, toshe magudanan ruwa da zubar da shara na daga cikin abubuwan da ke haddasa ambaliyar ruwa a Abuja. Wike ya kuma umarci hukumomin FCT da su gaggauta kwashe laka da datti daga magudanan ruwa a babban birnin,  Ya ce sauyin yanayi da yawan ruwan sama na taka rawa wajen ambaliyar, amma ayyukan mutane ma na kara tsananta matsalar. Ministan ya ce ba za a dakatar da rushe-rushen saboda ana cikin lokacin siyasa ba, yana mai cewa gwamnati na da niyyar tabbatar da dokokin tsara birnin.

Daga yanzu ‘Daukar doka a hannu’ daidai yake da kisan kai — IGP Disu ya gargadi ’yan Najeriya

Ya gargadi mutanen da ke shirya ko tunzura jama'a, wadanda ke daukar hotuna ko bidiyon abin da ke faruwa su yada shi, da kuma wadanda ke hana ’yan sanda shiga tsakani ko kai agajin gaggawa kan wanda ake zargi, cewa su ma za su iya fuskantar tuhuma.

Ya Allah Ka Kare Mu Daga Maza Azzalumai – labarin wata maijego da na gani a asibiti ya girgiza ni

Ta haihu babu ko tsinke na haiuwa daga mijin, ya ki rako ta Asibiti, babu wani nashi kuma ko sisi bai bayar ba, ita ce matar shi ta huɗu, haihuwa na 11, yan uwanta suke komai, tana cikin nakuda ma sai da tayi mashi tuwo kafin ta taho Asibiti....

Fitaccen Jarumin Fim Nicolas Cage Ya Ce Yana Iya Tuna Abin da Ya Faru Tun Yana Cikin Mahaifiyarsa

Masana kimiyya sun ce yawancin mutane ba sa iya tuna abubuwan da suka faru kafin su kai kusan shekara biyu ko uku

Adeleke ya sake lashe zaben gwamnan Osun, ya doke Oyebamiji

Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 511,067, inda ya doke dan takarar APC, Bola Oyebamiji, wanda ya samu kuri’u 444,815.

Rayuwar Alkali Bunza a Hannun Masu Garkuwa: Ya Ce Ya Yi Tafiyar Kilomita 25 Ba Takalmi

Ya kuma ce abin da ya faru da shi ya kara tabbatar masa da bukatar gwamnati ta magance matsalolin talauci, rashin aikin yi da karancin ilimi, wadanda ya ce suna taimakawa wajen yaduwar ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

“Ashe ’Yan Arewa Mutanen Kirki Ne Haka?” – Inyamura Ta Yi Mamaki Bayan Direban Keke Ya Mayar Mata da Wayarta da Ta Manta

Chioma ta ce abin ya matukar burge ta, musamman da ta gano cewa Mohammed bai taba mallakar ko amfani da wayar Android ba, amma duk da haka ya mayar da wayar da ta fada hannunsa
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img