“Ashe ’Yan Arewa Mutanen Kirki Ne Haka?” – Inyamura Ta Yi Mamaki Bayan Direban Keke Ya Mayar Mata da Wayarta da Ta Manta
Daga Wakiliya
Wata mata mai suna Chioma Anyanwu ta bayyana yadda wani direban babur mai kafa uku, wato Keke Napep (A daidaita Sahu), mai suna Mohammed ya mayar mata da wayarta da ta manta a cikin babur dinsa.
Chioma ta ce ba ta taba sanin Mohammed ba kafin ranar da ya dauke ta a matsayin fasinja a safiyar ranar.
Ta ce bayan ta isa inda za ta sauka, ta biya Mohammed naira 1,000, inda ya mayar mata da ragowar canjin ta, sannan suka rabu.
Sai dai bayan kusan mintuna biyar, Chioma ta gano cewa wayarta da ta saka a aljihun rigarta ba ta nan.
Ta ce ta fara tunanin ko ta bar wayar a wurin da ta je, amma daga baya wani abokin aikinta ya kira lambarta, sai wani mutum mai magana da harshen Hausa ya daga wayar.
A cewar Chioma, mutumin ya tabbatar da cewa wayar tana hannunsa, kuma ya ce zai dawo da ita.
Bayan wani lokaci, Mohammed ya isa wajen ofishin Chioma a cikin ruwan sama, dauke da fasinjoji, sannan ya mika mata wayarta.
Chioma ta ce abin ya matukar burge ta, musamman da ta gano cewa Mohammed bai taba mallakar ko amfani da wayar Android ba, amma duk da haka ya mayar da wayar da ta fada hannunsa.
Ta yaba wa Mohammed kan gaskiya da amana, inda ta ce lamarin ya kara tabbatar mata da cewa mutanen kirki suna cikin al'umma ba tare da la’akari da kabila ko addini ba.
Ta kuma yi masa addu’ar samun albarka da nasara, tare da cewa Mohammed ya zama kamar dan uwanta saboda irin abin kirkin da ya yi mata.





