Tinubu ya amince da ƙarin albashi ga jami’an sojin Najeriya
Daga Wakiliya
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙarin albashi ga jami’an rundunar sojin Najeriya da ya kai tsakanin kashi 30 zuwa 80 cikin ɗari, a wani mataki da gwamnatin tarayya ta ce na inganta jin daɗin dakarun ƙasar.
Sanarwar da Fadar Shugaban Ƙasa ta fitar ta ce kusan jami’ai da sojoji 250,000 ne za su amfana da sabon tsarin albashin, wanda zai fara aiki daga ranar 1 ga Satumban 2026.
A ƙarƙashin sabon tsarin, manyan jami’an da ke sama da muƙamin Kanal, ciki har da Birgediya Janar, Manjo Janar, Laftanar Janar da Janar, za su samu ƙarin albashi na kashi 30 cikin ɗari.
Jami’an da ke daga muƙamin Kanal zuwa Warrant Officer kuwa za su samu ƙarin albashi na kashi 50 cikin ɗari, yayin da sojoji daga muƙamin Private zuwa Staff Sergeant za su samu ƙarin albashi mafi yawa, wato kashi 80 cikin ɗari.
Fadar Shugaban Ƙasa ta ce sabon tsarin zai ƙara kuɗin albashin sojojin Najeriya na shekara daga naira biliyan 660 zuwa naira biliyan 924.
A cewar Shugaba Tinubu, gwamnatinsa na ci gaba da yaba wa jajircewa da sadaukarwar jami’an tsaro wajen yaƙi da ta’addanci, garkuwa da mutane da kuma ‘yan bindiga a sassa daban-daban na ƙasar.
Ya ce dole ne gwamnati ta tallafa wa waɗanda ke sadaukar da rayuwarsu domin kare lafiya da dukiyoyin ‘yan Najeriya, yana mai jaddada cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da ba rundunar soji kayan aiki na zamani da kuma inganta walwalarsu.
Shugaban ya kuma bayyana cewa babu wata ƙasa da za ta iya samun ci gaba ba tare da ingantaccen tsaro ba, yana mai cewa gwamnati za ta ci gaba da amfani da dukkanin ƙarfin rundunonin tsaro domin murƙushe barazanar tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Tinubu ya kuma buƙaci jami’an sojin su ɗauki wannan ƙarin albashi a matsayin wata alama ta godiyar gwamnati bisa hidimar da suke yi wa ƙasa, yana mai bayyana fatan cewa tare za su yi nasara a kan masu neman tayar da zaune tsaye a Najeriya.




