Adeleke ya sake lashe zaben gwamnan Osun, ya doke Oyebamiji
Daga Wakiliya
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta ayyana Gwamnan Jihar Osun, Ademola Adeleke, a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar da aka gudanar a shekarar 2026.
Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 511,067, inda ya doke dan takarar APC, Bola Oyebamiji, wanda ya samu kuri’u 444,815.
Dan takarar ADC ya samu kuri’u 17,180.
A cewar sakamakon karshe da aka sanar, an yi wa masu kada kuri’a 2,339,544 rajista, yayin da aka tantance 1,010,684 daga cikinsu.
Jimillar kuri’un da aka kada ta kai 1,005,800, yayin da kuri’u 20,721 aka soke.
An sanya hannu tare da hatimce sakamakon da jami’in tattara sakamakon zaben, Farfesa Joshua Olalekan Ogunwole.
Wannan nasara ta bai wa Ademola Adeleke damar ci gaba da jagorantar jihar Osun a wa’adinsa na biyu.




