Daga yanzu ‘Daukar doka a hannu’ kisan kai ne — IGP Disu ya gargadi ’yan Najeriya
Daga Wakiliya
Sufeto-Janar na ’Yan Sandan Najeriya, IGP Tunde Disu, ya gargadi ’yan Najeriya kan daukar doka a hannu, yana mai cewa duk wanda ya kai wa wanda ake zargi hari ko ya kashe shi ta hanyar yi wa wanda ake zargin taron dangi zai fuskanci tuhumar kisan kai.
IGP Tunde Disu ya ce an dauki matakin ne domin dakile karuwar kashe mutane ba bisa ka’ida ba da ake samu a sassan kasar.
A cikin wani faifan bidiyo da ya yadu a kafafen sada zumunta, IGP Tunde Disu ya ce ya umurci kwamishinonin ’yan sanda na jihohi 36 da kuma Abuja da su dauki duk lamari da ya kai ga kisa a matsayin homicide, tare da gudanar da cikakken bincike.
Ya ce dokokin Najeriya sun tanadi hukunci mai tsauri kan kisan kai, inda ya ambaci Sashe na 319 na Criminal Code da Sashe na 221 na Penal Code.
“Duk wanda ya kai wa wanda ake zargi hari ko ya kashe shi yana da laifin kisan kai,” in ji shi.
IGP Disu ya kuma ce laifin ba zai tsaya kan wadanda suka aikata kisan kai kawai ba.
Ya gargadi mutanen da ke shirya ko tunzura jama'a, wadanda ke daukar hotuna ko bidiyon abin da ke faruwa su yada shi, da kuma wadanda ke hana ’yan sanda shiga tsakani ko kai agajin gaggawa kan wanda ake zargi, cewa su ma za su iya fuskantar tuhuma.
Ya ce Sashe na 516 na Criminal Code ya tanadi hukunci kan hada baki wajen aikata laifi, ciki har da makircin kisan kai.
Gargadin na IGP Tunde Disu ya zo ne a daidai lokacin da ake ta yada wasu bidiyoyin mutane na daukar doka a hannu kan mutanen da ake zargi da aikata laifuka.
Daya daga cikin irin wadannan hare-haren shi ne wanda ya yi sanadin mutuwar Ibrahim Mbaya, wanda aka fi sani da Ibee, wani matashin da ya kammala karatu a Jami’ar Jos. An kai masa hari a Jos bayan zargin cewa ya saci wayar iPhone 12, lamarin da ya kai ga mutuwarsa.
’Yan sanda sun ce an kama wasu mutane dangane da lamarin.
IGP Tunde Disu ya bukaci ’yan Najeriya da su daina daukar doka a hannunsu, su rika mika duk wanda ake zargi da aikata laifi ga jami’an tsaro domin gudanar da bincike da daukar matakin da ya dace.
Ya ce rundunar ’yan sandan Najeriya ba za ta kyale wadanda ke da hannu wajen kashe mutane ta hanyar ‘jungle justice ko daukar doka a hannu’ ba, tare da alkawarin gurfanar da wadanda aka samu da laifi a gaban kotu.




