APC ta zargi an yi mata magudin zaɓe a Osun, ta nemi a sake duba sakamakon
Daga Wakiliya
Jam’iyyar APC a jihar Osun ta ce akwai abubuwan da ke nuna an yi mata magudi a zaɓen gwamnan jihar da aka gudanar ranar Asabar, inda ta nemi a sake duba sakamakon zaɓen.
Ɗan takarar jam’iyyar APC, Bola Oyebamiji, wanda ya zo na biyu da ƙuri’a 444,815, ya ce yana goyon bayan matakin jam’iyyar na yin bitar sakamakon zaɓen.
Jam’iyyar Accord ce ta lashe zaɓen, inda gwamna Ademola Adeleke ya samu ƙuri’a 511,067, yayin da ɗan takarar ADC, Najeem Salaam, ya zo na uku da ƙuri’a 17,180.
A cikin wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X ranar Talata, Bola Oyebamiji ya ce duk da cewa yana mutunta matakin da aka sanar, yana goyon bayan shawarar APC na sake duba yadda zaɓen ya gudana da sakamakonsa.
Ya kuma gode wa magoya bayansa da suka mara masa baya, tare da kira gare su da su kasance cikin natsuwa da zaman lafiya bayan zaɓen.
Sai dai Oyebamiji ya ce akwai ƙarin hare-hare kan mambobin APC da magoya bayansa, yana mai kira ga Rundunar ’Yan Sandan Najeriya da sauran hukumomin tsaro da su gaggauta ɗaukar mataki.
Ya ce duk da kammala zaɓen, APC da magoya bayansa za su ci gaba da fafutukar ganin an samu ci gaba mai inganci da haɗin kai a jihar.
A ranar Lahadi ne jami’in INEC mai bayyana sakamakon zaɓen, Joshua Ogunwole, ya ayyana Ademola Adeleke a matsayin wanda ya lashe zaɓen, bayan ya samu ƙuri’a 511,067.
Sai dai APC ta ce tana ci gaba da duba sakamakon da yadda aka gudanar da zaɓen, wanda zai iya zama matakin farko na ƙalubalantar sakamakon da aka sanar.




