Rayuwar Alkali Bunza a Hannun Masu Garkuwa: Ya Ce Ya Yi Tafiyar Kilomita 25 Ba Takalmi

Rayuwar Alkali Bunza a Hannun Masu Garkuwa: Ya Ce Ya Yi Tafiyar Kilomita 25 Ba Takalmi – Yan bindiga matsorata ne!

Daga Wakiliya

Alƙalin Babbar Kotun Jihar Kebbi, Mai Shari’a Faruk Hassan Bunza, ya bayyana irin wahalhalun da ya fuskanta a tsawon kwanaki tara da ya yi a hannun masu garkuwa da mutane.

Mai Shari’a Bunza ya ce masu garkuwar sun yi tafiya da shi mai nisan kusan kilomita 25 ba takalmi, kafin daga bisani su hau babura zuwa inda suke tsare mutane.

Ya ce an sace shi ne daga gidansa a garin Bunza a ranar 26 ga Yuli, sannan aka sake shi a ranar 3 ga Agusta bayan an biya kudin fansa.

A cewar Mai Shari’a Bunza, masu garkuwar sun kai shi wani sansani da ke Dutsen Bandan a yankin Dakin Gari, inda ya shafe kwanaki tara.

Ya ce bayan isarsa sansanin, an tambaye shi irin abincin da yake so, inda ya zabi tuwon shinkafa ko semo da miyar kubewa.

Mai Shari’a Bunza ya ce ana ba shi abinci sau biyu a rana tare da ruwan kwalba da Maltina.

Sai dai ya ce wasu mutane biyu da aka sace tare da shi ba su samu irin wannan kulawar ba, domin a cewarsa, ba a ba su abinci mai kyau, yayin da ake ba su ruwan rafi idan sun nemi ruwan sha.

Ya bayyana cewa masu garkuwar ba su yi masa duka ko wani mummunan cin zarafi ba, amma dai a kodayaushe suna dauke da makamai kuma suna cikin fargaba a kodayaushe.

Mai Shari’a Bunza ya ce ya yi imanin cewa an sace shi ne domin neman kudin fansa, musamman saboda matsayinsa na alkali da kuma bayanan da masu garkuwar suka ce sun samu game da dukiyarsa.

Ya ce daga baya masu garkuwar sun gudu sun bar shi shi kadai a sansanin bayan sun karbi kudin fansa, lamarin da ya ba shi damar tserewa.

Bunza ya ce bayan ya gane cewa babu mai tsaron sa, ya cire abin da aka rufe masa fuska da shi sannan ya sauko daga kan tsaunin, inda ya ci gaba da tafiya har ya isa wani kauye.

Daga bisani ya samu abin hawa da ya kai shi gida, inda iyalansa da al’ummar garin suka yi murna sosai da ganin dawowarsa.

Mai Shari’a Bunza ya yi amfani da wannan dama wajen yin kira ga gwamnati da ta kara tsaron alkalai, musamman wadanda ke jagorantar shari’o’in da suka shafi ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

Ya ce duk da abin da ya faru da shi, lamarin ba zai sa ya daina aikinsa na shari’a ba.

“A duniyar nan babu abin da zai sauya halina da jajircewata wajen gudanar da aikina na alkali,” in ji shi.

Ya kuma ce abin da ya faru da shi ya kara tabbatar masa da bukatar gwamnati ta magance matsalolin talauci, rashin aikin yi da karancin ilimi, wadanda ya ce suna taimakawa wajen yaduwar ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

DA DUMI-DUMI

Adeleke ya sake lashe zaben gwamnan Osun, ya doke Oyebamiji

Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 511,067, inda ya doke dan takarar APC, Bola Oyebamiji, wanda ya samu kuri’u 444,815.

“Ashe ’Yan Arewa Mutanen Kirki Ne Haka?” – Inyamura Ta Yi Mamaki Bayan Direban Keke Ya Mayar Mata da Wayarta da Ta Manta

Chioma ta ce abin ya matukar burge ta, musamman da ta gano cewa Mohammed bai taba mallakar ko amfani da wayar Android ba, amma duk da haka ya mayar da wayar da ta fada hannunsa

Matafiya A Kula: Hanyar Abuja – Kaduna ta toshe gaba ɗaya a daren nan

Masu tafiya zuwa Abuja ko Kaduna su kula, su kuma yaɗa wannan saƙo domin sauran matafiya su sani 

Bayani Dalla-dalla yadda za ku yi rajistar sunan kasuwancin ku a CAC Kyauta

Kada ka biya kowa kuɗi domin wannan rajista. Gwamnati ta ce CAC ba za ta karɓi kuɗin rajistar wannan shirin ba. Haka kuma, ka yi hattara da masu damfara da ke cewa za su gaggauta maka rajista idan ka biya su kuɗi.

Abubuwa 6 da ya kamata a yi kafin ƙarfe 9 na safe domin rage haɗarin shanyewar ɓarin jiki

Shan magunguna yadda likita ya umarta, rage damuwa, motsa jiki, cin abinci mai kyau da kuma guje wa taba da vape na daga cikin matakan da za su taimaka wajen kula da lafiyar zuciya da jijiyoyin jini.

Kanun Labarai

Adeleke ya sake lashe zaben gwamnan Osun, ya doke Oyebamiji

Ademola Adeleke na jam’iyyar PDP ya samu kuri’u 511,067, inda ya doke dan takarar APC, Bola Oyebamiji, wanda ya samu kuri’u 444,815.

“Ashe ’Yan Arewa Mutanen Kirki Ne Haka?” – Inyamura Ta Yi Mamaki Bayan Direban Keke Ya Mayar Mata da Wayarta da Ta Manta

Chioma ta ce abin ya matukar burge ta, musamman da ta gano cewa Mohammed bai taba mallakar ko amfani da wayar Android ba, amma duk da haka ya mayar da wayar da ta fada hannunsa

Matafiya A Kula: Hanyar Abuja – Kaduna ta toshe gaba ɗaya a daren nan

Masu tafiya zuwa Abuja ko Kaduna su kula, su kuma yaɗa wannan saƙo domin sauran matafiya su sani 

Bayani Dalla-dalla yadda za ku yi rajistar sunan kasuwancin ku a CAC Kyauta

Kada ka biya kowa kuɗi domin wannan rajista. Gwamnati ta ce CAC ba za ta karɓi kuɗin rajistar wannan shirin ba. Haka kuma, ka yi hattara da masu damfara da ke cewa za su gaggauta maka rajista idan ka biya su kuɗi.

Abubuwa 6 da ya kamata a yi kafin ƙarfe 9 na safe domin rage haɗarin shanyewar ɓarin jiki

Shan magunguna yadda likita ya umarta, rage damuwa, motsa jiki, cin abinci mai kyau da kuma guje wa taba da vape na daga cikin matakan da za su taimaka wajen kula da lafiyar zuciya da jijiyoyin jini.

Zaɓen Osun: Mutum 75 cikin masu zaɓe 342 ne suka kada kuri’a a wata rumfar zabe saboda matsalar BVAS

Wani jami’in INEC da ke aikin zaɓen a rumfar ya tabbatar da samun jinkirin, yana mai cewa ana ƙoƙarin magance matsalar na’urar tare da ci gaba da tantance masu zaɓen da ba su samu damar kammala aikin ba.

Adam A. Zango ya sake aure a Jamhuriyar Nijar – Ya Auri Mamah

Adam A. Zango ya sake aure a Jamhuriyar Nijar...

An kama wata Amarya bisa zargin sanya wa mijinta guba kwana 40 da aurensu a Bauchi

Lamarin ya faru ne a ranar Laraba, 12 ga watan Agustan 2026, da misalin karfe 3:15 na rana a kauyen Gwamma da ke karamar hukumar Bauchi.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img