UAE Za Ta Zuba Jarin Dala Biliyan $71 a Afirka, Domin Zurfafa Haɗin Gwiwa da Nahiyar
Daga Wakiliya
WAKILIYA – Ƙasar Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa (UAE) ta bayyana cewa za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarta da ƙasashen Afirka, inda ta fi mayar da hankali kan makamashi mai tsafta, gine-ginen more rayuwa da kuma fasahar zamani domin bunƙasa tattalin arzikin nahiyar.
Ministan Ƙasa na UAE, Saeed bin Mubarak Al Hajeri, ya ce ƙasarsa na kallon Afirka a matsayin muhimmiyar abokiyar hulɗa a shirinta na faɗaɗa tattalin arziƙi da rage dogaro da man fetur.
Al Hajeri ya bayyana cewa tsakanin shekarun 2021 zuwa 2025, UAE ta zuba kusan dala biliyan 71.32 a ƙasashen yankin Hamada (Sub-Saharan Africa).
Ya ƙara da cewa UAE ta ware sama da dala biliyan 70 domin ayyukan makamashi mai tsafta da kore a faɗin nahiyar, ta hannun shirye-shirye irin su Masdar da kuma dandalin Etihad 7.
A cewarsa, ƙasar na kuma ƙara zuba jari a fannin hanyoyi, tashoshin jiragen ruwa da dabarun sufuri ta hanyar kamfanonin DP World, AD Ports Group, da kuma tallafin Abu Dhabi Fund for Development.
Ministan ya ce waɗannan jarin za su taimaka wajen rage tsadar kasuwanci, inganta hanyoyin sufuri, faɗaɗa samar da wutar lantarki, samar da ayyukan yi da kuma inganta musayar fasaha da ƙwarewa tsakanin UAE da ƙasashen Afirka.
Ya kuma bayyana cewa UAE ta rattaba hannu kan yarjejeniyoyin haɗin gwiwar tattalin arziƙi guda tara da ƙasashen Afirka, tare da burin kai cinikayyar ƙetare ta ƙasar zuwa dirham tiriliyan huɗu (AED4tn) nan da shekarar 2031.
Bugu da ƙari, Al Hajeri ya ce UAE ta ƙaddamar da wani shiri na dala biliyan ɗaya domin bunƙasa fasahar Basirar Wucin Gadi (AI) a Afirka, wanda aka sanar da shi a taron G20 da aka gudanar a Afirka ta Kudu.
Ya jaddada cewa UAE za ta ci gaba da aiki tare da gwamnatocin Afirka da kamfanoni masu zaman kansu wajen aiwatar da ayyukan da za su haɓaka ci gaba mai ɗorewa da samar da damarmakin tattalin arziƙi ga nahiyar.





