2027: Matasan APC na Arewa Sun Yi Barazanar Janye Goyon Baya Ga Tinubu, Saboda Zargi Ana Nuna Musu Wariya

Daga Wakiliya

Wasu ƙungiyoyin matasan jam’iyyar APC daga Arewacin Najeriya sun yi barazanar janye goyon bayansu ga takarar Shugaba Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027 idan ba a magance abin da suka kira nuna musu wariya da rashin ba su damar shiga harkokin siyasa ba.

Barazanar ta biyo bayan wata ganawa da ta haɗa North-West APC Youth Stakeholders Forum, ƙarƙashin jagorancin Bashir Ruma, da Arewa Democratic Youth Stakeholders Forum.

A cikin wata sanarwa da Sakataren Yaɗa Labarai na ƙungiyar, Salawudeen Shaibu Planner, ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta ce an ware matasan Arewa daga muƙaman siyasa, shugabancin matasa da kuma yanke muhimman shawarwari a cikin jam’iyyar APC da gwamnatin tarayya.

Ƙungiyar ta ce za ta fara tattara ƙungiyoyin magoya bayan APC a faɗin Arewa domin adawa da abin da ta bayyana a matsayin rashin adalci da siyasar nuna bambancin yanki.

Har ila yau, ta naɗa Haruna Sardauna a matsayin mai kula da yankin Arewa maso Gabas, yayin da aka naɗa Idiriss Jibrin domin jagorantar yankin Arewa ta Tsakiya.

Ƙungiyar ta kuma yi zargin cewa ɗan Shugaba Tinubu, Seyi Tinubu, na da tasiri wajen naɗe-naɗen matasa da shugabanci, inda ta ce ana fifita mutanen Kudu maso Yamma, musamman Yarabawa, lamarin da ta ce ya sa matasan Arewa ke jin an mayar da su saniyar ware.

Ta ambaci Ma’aikatar Raya Matasa, shugabancin matasan APC, NANS, NYCN da sauran ƙungiyoyin matasa a matsayin wuraren da ta ce ana samun rashin daidaito.

Haka kuma, ƙungiyar ta yi zargin cewa ƙungiyoyin City Boy Movement da Relax, Tinubu Is Fixing Nigeria Movement sun samu fifiko saboda alaƙarsu da Seyi Tinubu, yayin da ake matsa wa ƙungiyoyin Arewa su yi aiki tare da su.

A cewar ƙungiyar, ta umarci shugabannin ƙungiyoyin goyon bayan APC 1,378 da ke jihohin Arewa 19 da Babban Birnin Tarayya Abuja su fara tattaunawa kan yiwuwar janye goyon baya ga takarar Tinubu ta wa’adi na biyu idan ba a saurari korafinsu ba.

Ƙungiyar ta jaddada cewa kuri’un Arewa sun taka muhimmiyar rawa wajen nasarar Tinubu a zaɓen 2023, don haka ta ce ya dace a bai wa yankin damar da ta dace a muƙamai da damar siyasa.

Duk da haka, Bashir Ruma ya buƙaci matasan Arewa su ci gaba da kasancewa masu zaman lafiya yayin da suke neman adalci da wakilci.

Ya zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, Fadar Shugaban Ƙasa, shugabancin APC na ƙasa da kuma Seyi Tinubu ba su fitar da wata sanarwa kan waɗannan zarge-zarge ba.

DA DUMI-DUMI

UAE Za Ta Zuba Jarin Dala Biliyan $71 a Afirka, Domin Zurfafa Haɗin Gwiwa da Nahiyar

Ya jaddada cewa UAE za ta ci gaba da aiki tare da gwamnatocin Afirka da kamfanoni masu zaman kansu wajen aiwatar da ayyukan da za su haɓaka ci gaba mai ɗorewa da samar da damarmakin tattalin arziƙi ga nahiyar.

Matsalar Rashin Amincewa Da Ke Hana Kasuwancin Intanet Bunƙasa a Najeriya Musamman Arewa

A yau, aika kuɗi ta banki ko manhajojin kuɗi ya zama abu mai sauƙi a Najeriya. Amma sauƙin tura kuɗi ba yana nufin an magance matsalar kasuwanci ba.

Kasar Guinea Ta Fice Daga Shirin Samar da Kuɗin Bai Ɗaya na ECOWAS -Ta Zabi Riƙe Kuɗinta

Ana sa ran shugabannin ECOWAS za su sake ganawa a watan Disamba domin tattauna sauran batutuwan da suka rage kafin fara amfani da kuɗin Eco.

Gaggawar Yaɗa Labaran da Ba a Tantance Ba Ka Iya Shafar Kasuwar Makamashi da Zuba Jari, Ya Jawo Tashin Farashi – NUPRC Ta Gargadi...

A ƙarshe, ta buƙaci 'yan jaridar da ke ba da rahotannin makamashi su mayar da hankali kan tantance bayanai, fahimtar alkaluma da kuma bayar da cikakken mahallin labari domin tabbatar da sahihanci da ƙarfafa amincewar jama'a.

Najeriya Ba Ta da Tattalin Kula da Abubuwan Da Aka Gina, Shi Yasa Kasar Ta Kasa Ci Gaba – Okonjo-Iweala

Mu a Najeriya ba mu da kyakkyawar al'adar kula da abubuwan da muka gina. Ni ma 'yar Najeriya ce, amma dole ne mu faɗi gaskiya," in ji ta.

Kanun Labarai

UAE Za Ta Zuba Jarin Dala Biliyan $71 a Afirka, Domin Zurfafa Haɗin Gwiwa da Nahiyar

Ya jaddada cewa UAE za ta ci gaba da aiki tare da gwamnatocin Afirka da kamfanoni masu zaman kansu wajen aiwatar da ayyukan da za su haɓaka ci gaba mai ɗorewa da samar da damarmakin tattalin arziƙi ga nahiyar.

Matsalar Rashin Amincewa Da Ke Hana Kasuwancin Intanet Bunƙasa a Najeriya Musamman Arewa

A yau, aika kuɗi ta banki ko manhajojin kuɗi ya zama abu mai sauƙi a Najeriya. Amma sauƙin tura kuɗi ba yana nufin an magance matsalar kasuwanci ba.

Kasar Guinea Ta Fice Daga Shirin Samar da Kuɗin Bai Ɗaya na ECOWAS -Ta Zabi Riƙe Kuɗinta

Ana sa ran shugabannin ECOWAS za su sake ganawa a watan Disamba domin tattauna sauran batutuwan da suka rage kafin fara amfani da kuɗin Eco.

Gaggawar Yaɗa Labaran da Ba a Tantance Ba Ka Iya Shafar Kasuwar Makamashi da Zuba Jari, Ya Jawo Tashin Farashi – NUPRC Ta Gargadi...

A ƙarshe, ta buƙaci 'yan jaridar da ke ba da rahotannin makamashi su mayar da hankali kan tantance bayanai, fahimtar alkaluma da kuma bayar da cikakken mahallin labari domin tabbatar da sahihanci da ƙarfafa amincewar jama'a.

Najeriya Ba Ta da Tattalin Kula da Abubuwan Da Aka Gina, Shi Yasa Kasar Ta Kasa Ci Gaba – Okonjo-Iweala

Mu a Najeriya ba mu da kyakkyawar al'adar kula da abubuwan da muka gina. Ni ma 'yar Najeriya ce, amma dole ne mu faɗi gaskiya," in ji ta.

Malamin da ya shiga siyasa, aka yi ƙwaramniyar siyasa da shi, ya fi malamin da ya zauna kan buzun yana yi wa ‘yan siyasa...

Malamin da ya shiga siyasa, aka yi ƙwaramniyar siyasa da shi, ya fi malamin da ya zauna kan buzun yana yi wa 'yan siyasa addu'a -Dr. Ahmed Gumi

An Kashe Biliyoyin Naira Amma Duk da Haka Cibiyoyin Lafiya 6,516 Sun Gagara Aiki a Najeriya; Arewa Ce Kan Gaba

Jihar Katsina ce ke da mafi yawan cibiyoyin da ba sa aiki da guda 442, sai Osun da 406, yayin da Benue ke da 343, Enugu 335, Adamawa 286, sannan Borno na cikin jerin jihohin da ke fuskantar matsala.
spot_img

Labarai masu alaka

Sauran bangarori

spot_imgspot_img